Hausa
Sorah Al-'alaq ( The Clot )

Verses Number 19

اقْرَأْ بِاسْمِ رَبِّكَ الَّذِي خَلَقَSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 1
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
خَلَقَ الإِنسَانَ مِنْ عَلَقٍSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 2
Ya hahitta mutum daga gudan jini.
اقْرَأْ وَرَبُّكَ الأَكْرَمُSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 3
Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.
الَّذِي عَلَّمَ بِالْقَلَمِSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 4
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
عَلَّمَ الإِنسَانَ مَا لَمْ يَعْلَمْSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 5
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
كَلاَّ إِنَّ الإِنسَانَ لَيَطْغَىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 6
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
أَن رَّآهُ اسْتَغْنَىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 7
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
إِنَّ إِلَى رَبِّكَ الرُّجْعَىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 8
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
أَرَأَيْتَ الَّذِي يَنْهَىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 9
Shin, kã ga wanda ke hana.
عَبْدًا إِذَا صَلَّىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 10
Bãwã idan yã yi salla?
أَرَأَيْتَ إِن كَانَ عَلَى الْهُدَىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 11
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
أَوْ أَمَرَ بِالتَّقْوَىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 12
Ko ya yi umurni da taƙawa?
أَرَأَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 13
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
أَلَمْ يَعْلَمْ بِأَنَّ اللَّهَ يَرَىSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 14
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
كَلاَّ لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًا بِالنَّاصِيَةِSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 15
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
نَاصِيَةٍ كَاذِبَةٍ خَاطِئَةٍSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 16
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
فَلْيَدْعُ نَادِيَهSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 17
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
سَنَدْعُ الزَّبَانِيَةَSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 18
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).
كَلاَّ لا تُطِعْهُ وَاسْجُدْ وَاقْتَرِبْSorah Al-'alaq ( The Clot ) Verse Number 19
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).