Hausa
Sorah Ad-Dhuha ( The Forenoon )

Verses Number 11

وَالضُّحَىSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da hantsi.
وَاللَّيْلِ إِذَا سَجَىSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 2
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 3
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
وَلَلآخِرَةُ خَيْرٌ لَّكَ مِنَ الأُولَىSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 4
Kuma lalle ta ƙarshe ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
وَلَسَوْفَ يُعْطِيكَ رَبُّكَ فَتَرْضَىSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 5
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
أَلَمْ يَجِدْكَ يَتِيمًا فَآوَىSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 6
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
وَوَجَدَكَ ضَالًّا فَهَدَىSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 7
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
وَوَجَدَكَ عَائِلا فَأَغْنَىSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 8
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
فَأَمَّا الْيَتِيمَ فَلا تَقْهَرْSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 9
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
وَأَمَّا السَّائِلَ فَلا تَنْهَرْSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 10
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
وَأَمَّا بِنِعْمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثْSorah Ad-Dhuha ( The Forenoon ) Verse Number 11
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).