Hausa
Sorah Al-Layl ( The Night )

Verses Number 21

وَاللَّيْلِ إِذَا يَغْشَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
وَالنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 2
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
وَمَا خَلَقَ الذَّكَرَ وَالأُنثَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 3
Da abin da ya halitta namiji da mace.
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 4
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
فَأَمَّا مَن أَعْطَى وَاتَّقَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 5
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
وَصَدَّقَ بِالْحُسْنَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 6
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْيُسْرَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 7
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
وَأَمَّا مَن بَخِلَ وَاسْتَغْنَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 8
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
وَكَذَّبَ بِالْحُسْنَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 9
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
فَسَنُيَسِّرُهُ لِلْعُسْرَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 10
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
وَمَا يُغْنِي عَنْهُ مَالُهُ إِذَا تَرَدَّىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 11
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 12
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya.
وَإِنَّ لَنَا لَلْآخِرَةَ وَالأُولَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 13
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 14
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.
لا يَصْلاهَا إِلاَّ الأَشْقَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 15
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa.
الَّذِي كَذَّبَ وَتَوَلَّىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 16
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya.
وَسَيُجَنَّبُهَا الأَتْقَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 17
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta.
الَّذِي يُؤْتِي مَالَهُ يَتَزَكَّىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 18
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka.
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 19
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta.
إِلاَّ ابْتِغَاء وَجْهِ رَبِّهِ الأَعْلَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 20
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka.
وَلَسَوْفَ يَرْضَىSorah Al-Layl ( The Night ) Verse Number 21
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi).