Hausa
Sorah Al-Balad ( The City )

Verses Number 20

لا أُقْسِمُ بِهَذَا الْبَلَدِSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 1
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.
وَأَنتَ حِلٌّ بِهَذَا الْبَلَدِSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 2
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
وَوَالِدٍ وَمَا وَلَدَSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 3
Da mahaifi da abin da ya haifa.
لَقَدْ خَلَقْنَا الإِنسَانَ فِي كَبَدٍSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 4
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 5
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالا لُّبَدًاSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 6
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"
أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُ أَحَدٌSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 7
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
أَلَمْ نَجْعَل لَّهُ عَيْنَيْنِSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 8
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
وَلِسَانًا وَشَفَتَيْنِSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 9
Da harshe, da leɓɓa biyu.
وَهَدَيْنَاهُ النَّجْدَيْنِSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 10
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?
فَلا اقْتَحَمَ الْعَقَبَةَSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 11
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْعَقَبَةُSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 12
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
فَكُّ رَقَبَةٍSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 13
Ita ce fansar wuyan bãwa.
أَوْ إِطْعَامٌ فِي يَوْمٍ ذِي مَسْغَبَةٍSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 14
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 15
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
أَوْ مِسْكِينًا ذَا مَتْرَبَةٍSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 16
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
ثُمَّ كَانَ مِنَ الَّذِينَ آمَنُوا وَتَوَاصَوْا بِالصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا بِالْمَرْحَمَةِSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 17
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
أُوْلَئِكَ أَصْحَابُ الْمَيْمَنَةِSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 18
Waɗannan ne ma'abũta albarka
وَالَّذِينَ كَفَرُوا بِآيَاتِنَا هُمْ أَصْحَابُ الْمَشْأَمَةِSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 19
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci
عَلَيْهِمْ نَارٌ مُّؤْصَدَةٌSorah Al-Balad ( The City ) Verse Number 20
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.