Hausa
Sorah Al-Fajr ( The Dawn )

Verses Number 30

وَالْفَجْرِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da alfijiri.
وَلَيَالٍ عَشْرٍSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 2
Da darũruwa gõma.
وَالشَّفْعِ وَالْوَتْرِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 3
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.
وَاللَّيْلِ إِذَا يَسْرِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 4
Da dare idan yana shũɗewa.
هَلْ فِي ذَلِكَ قَسَمٌ لِّذِي حِجْرٍSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 5
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?
أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 6
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?
إِرَمَ ذَاتِ الْعِمَادِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 7
Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.
الَّتِي لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِي الْبِلادِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 8
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).
وَثَمُودَ الَّذِينَ جَابُوا الصَّخْرَ بِالْوَادِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 9
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?
وَفِرْعَوْنَ ذِي الأَوْتَادِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 10
Da Fir'auna mai turãku.
الَّذِينَ طَغَوْا فِي الْبِلادِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 11
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?
فَأَكْثَرُوا فِيهَا الْفَسَادَSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 12
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.
فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 13
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.
إِنَّ رَبَّكَ لَبِالْمِرْصَادِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 14
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.
فَأَمَّا الإِنسَانُ إِذَا مَا ابْتَلاهُ رَبُّهُ فَأَكْرَمَهُ وَنَعَّمَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَكْرَمَنِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 15
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."
وَأَمَّا إِذَا مَا ابْتَلاهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُ فَيَقُولُ رَبِّي أَهَانَنِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 16
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."
كَلاَّ بَل لّا تُكْرِمُونَ الْيَتِيمَSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 17
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!
وَلا تَحَاضُّونَ عَلَى طَعَامِ الْمِسْكِينِSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 18
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!
وَتَأْكُلُونَ التُّرَاثَ أَكْلا لَّمًّاSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 19
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.
وَتُحِبُّونَ الْمَالَ حُبًّا جَمًّاSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 20
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.
كَلاَّ إِذَا دُكَّتِ الأَرْضُ دَكًّا دَكًّاSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 21
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.
وَجَاءَ رَبُّكَ وَالْمَلَكُ صَفًّا صَفًّاSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 22
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.
وَجِيءَ يَوْمَئِذٍ بِجَهَنَّمَ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ الإِنسَانُ وَأَنَّى لَهُ الذِّكْرَىSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 23
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!
يَقُولُ يَا لَيْتَنِي قَدَّمْتُ لِحَيَاتِيSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 24
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"
فَيَوْمَئِذٍ لّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُ أَحَدٌSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 25
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.
وَلا يُوثِقُ وَثَاقَهُ أَحَدٌSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 26
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.
يَا أَيَّتُهَا النَّفْسُ الْمُطْمَئِنَّةُSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 27
Yã kai rai mai natsuwa!
ارْجِعِي إِلَى رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةًSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 28
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).
فَادْخُلِي فِي عِبَادِيSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 29
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).
وَادْخُلِي جَنَّتِيSorah Al-Fajr ( The Dawn ) Verse Number 30
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).