Hausa
Sorah At-Tariq ( The Night-Comer )

Verses Number 17

وَالسَّمَاء وَالطَّارِقِSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الطَّارِقُSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 2
To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?
النَّجْمُ الثَّاقِبُSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 3
Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.
إِن كُلُّ نَفْسٍ لَّمَّا عَلَيْهَا حَافِظٌSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 4
Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.
فَلْيَنظُرِ الإِنسَانُ مِمَّ خُلِقَSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 5
To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?
خُلِقَ مِن مَّاء دَافِقٍSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 6
An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.
يَخْرُجُ مِن بَيْنِ الصُّلْبِ وَالتَّرَائِبِSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 7
Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.
إِنَّهُ عَلَى رَجْعِهِ لَقَادِرٌSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 8
Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.
يَوْمَ تُبْلَى السَّرَائِرُSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 9
Rãnar da ake jarrabawar asirai.
فَمَا لَهُ مِن قُوَّةٍ وَلا نَاصِرٍSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 10
Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya kãre shi daga azãbar Allah).
وَالسَّمَاء ذَاتِ الرَّجْعِSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 11
Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.
وَالأَرْضِ ذَاتِ الصَّدْعِSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 12
Da ƙasa ma'abũciyar tsãgẽwa,
إِنَّهُ لَقَوْلٌ فَصْلٌSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 13
Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki
وَمَا هُوَ بِالْهَزْلِSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 14
Kuma shĩ bã bananci bane
إِنَّهُمْ يَكِيدُونَ كَيْدًاSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 15
Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.
وَأَكِيدُ كَيْدًاSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 16
Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.
فَمَهِّلِ الْكَافِرِينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْدًاSorah At-Tariq ( The Night-Comer ) Verse Number 17
Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.