Hausa
Sorah Al-Burooj ( The Big Stars )

Verses Number 22

وَالسَّمَاء ذَاتِ الْبُرُوجِSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da sama mai taurãrin lissafin shekara.
وَالْيَوْمِ الْمَوْعُودِSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 2
Da yinin da aka yi alkawarin zuwansa,
وَشَاهِدٍ وَمَشْهُودٍSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 3
Da yini mai shaidu, da yini da ake halarta a cikinsa
قُتِلَ أَصْحَابُ الأُخْدُودِSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 4
An la'ani mutãnen rãmi.
النَّارِ ذَاتِ الْوَقُودِSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 5
Wato wuta wadda aka hura.
إِذْ هُمْ عَلَيْهَا قُعُودٌSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 6
A lõkacin da suke a kan (gefen) ta a zazzaune.
وَهُمْ عَلَى مَا يَفْعَلُونَ بِالْمُؤْمِنِينَ شُهُودٌSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 7
Alhãli sũ, bisa ga abin da suke aikatãwa ga mũminai, sunã halarce.
وَمَا نَقَمُوا مِنْهُمْ إِلاَّ أَن يُؤْمِنُوا بِاللَّهِ الْعَزِيزِ الْحَمِيدِSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 8
Kuma ba su tuhumce su ba, fãce kawai domin sun yi ĩmãni da Allah Mabuwãyi, wanda ake gõdewa.
الَّذِي لَهُ مُلْكُ السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ وَاللَّهُ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ شَهِيدٌSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 9
Wanda Yake shi ne da mulkin sammai da ƙasa, kuma Allah a kan kõme halarce Yake.
إِنَّ الَّذِينَ فَتَنُوا الْمُؤْمِنِينَ وَالْمُؤْمِنَاتِ ثُمَّ لَمْ يَتُوبُوا فَلَهُمْ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمْ عَذَابُ الْحَرِيقِSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 10
Lalle ne waɗanda suka fitini mũminai maza da mũminai mãta, sa'an nan ba su tũba ba to, sunã da azãbar Jahannama, kuma sunã da azãbar gõbara.
إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ جَنَّاتٌ تَجْرِي مِن تَحْتِهَا الأَنْهَارُ ذَلِكَ الْفَوْزُ الْكَبِيرُSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 11
Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashin gidãjen. Wancan abu fa shi ne rabo babba.
إِنَّ بَطْشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 12
Lalle ne damƙar Ubangijinka mai tsanani ce ƙwarai.
إِنَّهُ هُوَ يُبْدِئُ وَيُعِيدُSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 13
Lalle ne Shĩ, Shi ne Mai ƙãga halitta, kuma Ya mayar da ita (bãyan mutuwa).
وَهُوَ الْغَفُورُ الْوَدُودُSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 14
Kuma Shi ne Mai gãfara, Mai bayyana sõyayya.
ذُو الْعَرْشِ الْمَجِيدُSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 15
Mai Al'arshi mai girma
فَعَّالٌ لِّمَا يُرِيدُSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 16
Mai aikatãwa ga abin da Yake nufi.
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ الْجُنُودِSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 17
Ko lãbãrin rundanõni yã zo maka.
فِرْعَوْنَ وَثَمُودَSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 18
Fir'auna da samũdãwa?
بَلِ الَّذِينَ كَفَرُوا فِي تَكْذِيبٍSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 19
Ã'aha! waɗanda suka kãfirta sunã cikin ƙaryatãwa.
وَاللَّهُ مِن وَرَائِهِم مُّحِيطٌSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 20
Alhãli, Allah daga bãyansu, Mai kẽwaye su ne (da saninSa).
بَلْ هُوَ قُرْآنٌ مَّجِيدٌSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 21
Ã'aha! Shi Alƙur'ãni ne mai girma.
فِي لَوْحٍ مَّحْفُوظٍSorah Al-Burooj ( The Big Stars ) Verse Number 22
A cikin Allo tsararre.