Hausa
Sorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder)

Verses Number 25

إِذَا السَّمَاء انشَقَّتْSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 1
Idan sama ta kẽce,
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 2
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
وَإِذَا الأَرْضُ مُدَّتْSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 3
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 4
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 5
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
يَا أَيُّهَا الإِنسَانُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَى رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلاقِيهِSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 6
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 7
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًاSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 8
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
وَيَنقَلِبُ إِلَى أَهْلِهِ مَسْرُورًاSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 9
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ وَرَاء ظَهْرِهِSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 10
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
فَسَوْفَ يَدْعُو ثُبُورًاSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 11
To, zã shi dinga kiran halaka!
وَيَصْلَى سَعِيرًاSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 12
Kuma ya shiga sa'ĩr.
إِنَّهُ كَانَ فِي أَهْلِهِ مَسْرُورًاSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 13
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
إِنَّهُ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 14
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
بَلَى إِنَّ رَبَّهُ كَانَ بِهِ بَصِيرًاSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 15
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
فَلا أُقْسِمُ بِالشَّفَقِSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 16
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
وَاللَّيْلِ وَمَا وَسَقَSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 17
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
وَالْقَمَرِ إِذَا اتَّسَقَSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 18
Da watã idan (haskensa) ya cika.
لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 19
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
فَمَا لَهُمْ لا يُؤْمِنُونَSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 20
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ الْقُرْآنُ لا يَسْجُدُونَSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 21
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
بَلِ الَّذِينَ كَفَرُواْ يُكَذِّبُونَSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 22
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
وَاللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 23
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 24
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
إِلاَّ الَّذِينَ آمَنُواْ وَعَمِلُواْ الصَّالِحَاتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍSorah Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) Verse Number 25
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.