Hausa
Sorah Al-Infitar ( The Cleaving )

Verses Number 19

إِذَا السَّمَاء انفَطَرَتْSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 1
Idan sama ta tsãge.
وَإِذَا الْكَوَاكِبُ انتَثَرَتْSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 2
Kuma idan taurãri suka wãtse.
وَإِذَا الْبِحَارُ فُجِّرَتْSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 3
Kuma idan tẽkuna aka facce su.
وَإِذَا الْقُبُورُ بُعْثِرَتْSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 4
Kuma idan kaburbura aka tõne su.
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 5
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.
يَا أَيُّهَا الإِنسَانُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ الْكَرِيمِSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 6
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci.
الَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّاكَ فَعَدَلَكَSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 7
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.
فِي أَيِّ صُورَةٍ مَّا شَاء رَكَّبَكَSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 8
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.
كَلاَّ بَلْ تُكَذِّبُونَ بِالدِّينِSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 9
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!
وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَافِظِينَSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 10
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.
كِرَامًا كَاتِبِينَSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 11
Mãsu daraja, marubũta.
يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 12
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.
إِنَّ الأَبْرَارَ لَفِي نَعِيمٍSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 13
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.
وَإِنَّ الْفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٍSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 14
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.
يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ الدِّينِSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 15
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.
وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَائِبِينَSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 16
Bã zã su faku daga gare ta ba.
وَمَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 17
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako?
ثُمَّ مَا أَدْرَاكَ مَا يَوْمُ الدِّينِSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 18
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?
يَوْمَ لا تَمْلِكُ نَفْسٌ لِّنَفْسٍ شَيْئًا وَالأَمْرُ يَوْمَئِذٍ لِلَّهِSorah Al-Infitar ( The Cleaving ) Verse Number 19
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.