Hausa
Sorah At-Takwir ( The Overthrowing )

Verses Number 29

إِذَا الشَّمْسُ كُوِّرَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 1
Idan rãna aka shafe haskenta
وَإِذَا النُّجُومُ انكَدَرَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 2
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
وَإِذَا الْجِبَالُ سُيِّرَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 3
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
وَإِذَا الْعِشَارُ عُطِّلَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 4
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
وَإِذَا الْوُحُوشُ حُشِرَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 5
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
وَإِذَا الْبِحَارُ سُجِّرَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 6
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
وَإِذَا النُّفُوسُ زُوِّجَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 7
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.
وَإِذَا الْمَوْؤُودَةُ سُئِلَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 8
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.
بِأَيِّ ذَنبٍ قُتِلَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 9
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
وَإِذَا الصُّحُفُ نُشِرَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 10
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
وَإِذَا السَّمَاء كُشِطَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 11
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
وَإِذَا الْجَحِيمُ سُعِّرَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 12
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
وَإِذَا الْجَنَّةُ أُزْلِفَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 13
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا أَحْضَرَتْSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 14
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
فَلا أُقْسِمُ بِالْخُنَّسِSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 15
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.
الْجَوَارِ الْكُنَّسِSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 16
Mãsu gudu suna ɓũya.
وَاللَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 17
Da dare idan ya bãyar da bãya.
وَالصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 18
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 19
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي الْعَرْشِ مَكِينٍSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 20
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
مُطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 21
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 22
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
وَلَقَدْ رَآهُ بِالأُفُقِ الْمُبِينِSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 23
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.
وَمَا هُوَ عَلَى الْغَيْبِ بِضَنِينٍSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 24
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَانٍ رَجِيمٍSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 25
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 26
Shin, a inã zã ku tafi?
إِنْ هُوَ إِلاَّ ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 27
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
لِمَن شَاء مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 28
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
وَمَا تَشَاؤُونَ إِلاَّ أَن يَشَاء اللَّهُ رَبُّ الْعَالَمِينَSorah At-Takwir ( The Overthrowing ) Verse Number 29
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.