Hausa
Sorah Abasa ( He frowned )

Verses Number 42

عَبَسَ وَتَوَلَّىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 1
Yã game huska kuma ya jũya bãya.
أَن جَاءَهُ الأَعْمَىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 2
Sabõda makãho yã je masa.
وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُ يَزَّكَّىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 3
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ الذِّكْرَىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 4
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
أَمَّا مَنِ اسْتَغْنَىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 5
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
فَأَنتَ لَهُ تَصَدَّىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 6
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
وَمَا عَلَيْكَ أَلاَّ يَزَّكَّىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 7
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
وَأَمَّا مَن جَاءَكَ يَسْعَىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 8
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
وَهُوَ يَخْشَىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 9
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 10
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
كَلاَّ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 11
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
فَمَن شَاء ذَكَرَهُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 12
Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).
فِي صُحُفٍ مُّكَرَّمَةٍSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 13
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
مَّرْفُوعَةٍ مُّطَهَّرَةٍSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 14
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
بِأَيْدِي سَفَرَةٍSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 15
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
كِرَامٍ بَرَرَةٍSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 16
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
قُتِلَ الإِنسَانُ مَا أَكْفَرَهُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 17
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
مِنْ أَيِّ شَيْءٍ خَلَقَهُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 18
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُ فَقَدَّرَهُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 19
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
ثُمَّ السَّبِيلَ يَسَّرَهُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 20
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
ثُمَّ أَمَاتَهُ فَأَقْبَرَهُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 21
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
ثُمَّ إِذَا شَاء أَنشَرَهُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 22
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
كَلاَّ لَمَّا يَقْضِ مَا أَمَرَهُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 23
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
فَلْيَنظُرِ الإِنسَانُ إِلَى طَعَامِهِSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 24
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
أَنَّا صَبَبْنَا الْمَاء صَبًّاSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 25
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
ثُمَّ شَقَقْنَا الأَرْضَ شَقًّاSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 26
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
فَأَنبَتْنَا فِيهَا حَبًّاSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 27
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
وَعِنَبًا وَقَضْبًاSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 28
Da inabi da ciyãwa.
وَزَيْتُونًا وَنَخْلاSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 29
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
وَحَدَائِقَ غُلْبًاSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 30
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
وَفَاكِهَةً وَأَبًّاSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 31
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
مَّتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 32
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
فَإِذَا جَاءَتِ الصَّاخَّةُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 33
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
يَوْمَ يَفِرُّ الْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 34
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
وَأُمِّهِ وَأَبِيهِSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 35
Da uwarsa da ubansa.
وَصَاحِبَتِهِ وَبَنِيهِSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 36
Da mãtarsa da ɗiyansa.
لِكُلِّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 37
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُّسْفِرَةٌSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 38
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
ضَاحِكَةٌ مُّسْتَبْشِرَةٌSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 39
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 40
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 41
Baƙi zai rufe su.
أُوْلَئِكَ هُمُ الْكَفَرَةُ الْفَجَرَةُSorah Abasa ( He frowned ) Verse Number 42
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).