Hausa
Sorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out )

Verses Number 46

وَالنَّازِعَاتِ غَرْقًاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 1
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
وَالنَّاشِطَاتِ نَشْطًاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 2
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
وَالسَّابِحَاتِ سَبْحًاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 3
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
فَالسَّابِقَاتِ سَبْقًاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 4
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.
فَالْمُدَبِّرَاتِ أَمْرًاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 5
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.
يَوْمَ تَرْجُفُ الرَّاجِفَةُSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 6
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
تَتْبَعُهَا الرَّادِفَةُSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 7
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 8
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
أَبْصَارُهَا خَاشِعَةٌSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 9
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
يَقُولُونَ أَئِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِي الْحَافِرَةِSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 10
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
أَئِذَا كُنَّا عِظَامًا نَّخِرَةًSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 11
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
قَالُوا تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 12
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 13
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
فَإِذَا هُم بِالسَّاهِرَةِSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 14
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ مُوسَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 15
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
إِذْ نَادَاهُ رَبُّهُ بِالْوَادِ الْمُقَدَّسِ طُوًىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 16
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
اذْهَبْ إِلَى فِرْعَوْنَ إِنَّهُ طَغَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 17
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَى أَن تَزَكَّىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 18
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
وَأَهْدِيَكَ إِلَى رَبِّكَ فَتَخْشَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 19
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"
فَأَرَاهُ الآيَةَ الْكُبْرَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 20
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.
فَكَذَّبَ وَعَصَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 21
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 22
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
فَحَشَرَ فَنَادَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 23
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
فَقَالَ أَنَا رَبُّكُمُ الأَعْلَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 24
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
فَأَخَذَهُ اللَّهُ نَكَالَ الآخِرَةِ وَالأُولَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 25
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
إِنَّ فِي ذَلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 26
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
أَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ السَّمَاء بَنَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 27
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 28
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 29
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
وَالأَرْضَ بَعْدَ ذَلِكَ دَحَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 30
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
أَخْرَجَ مِنْهَا مَاءَهَا وَمَرْعَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 31
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
وَالْجِبَالَ أَرْسَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 32
Da duwatsu, Yã kafe ta.
مَتَاعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَامِكُمْSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 33
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 34
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ الإِنسَانُ مَا سَعَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 35
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِمَن يَرَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 36
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
فَأَمَّا مَن طَغَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 37
To, amma wanda ya yi girman kai.
وَآثَرَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 38
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
فَإِنَّ الْجَحِيمَ هِيَ الْمَأْوَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 39
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ وَنَهَى النَّفْسَ عَنِ الْهَوَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 40
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
فَإِنَّ الْجَنَّةَ هِيَ الْمَأْوَىSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 41
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
يَسْأَلُونَكَ عَنِ السَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 42
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 43
Me ya haɗã ka da ambatonta?
إِلَى رَبِّكَ مُنتَهَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 44
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
إِنَّمَا أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 45
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوا إِلاَّ عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاهَاSorah An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) Verse Number 46
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.