Hausa
Sorah Al-Qiyamah ( The Resurrection )

Verses Number 40

لا أُقْسِمُ بِيَوْمِ الْقِيَامَةِSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 1
Bã sai Nã yi rantsuwa da Rãnar ¡iyãma ba.
وَلا أُقْسِمُ بِالنَّفْسِ اللَّوَّامَةِSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 2
Bã sai Nã yi rantsuwa da rai mai yawan zargin kansa ba.
أَيَحْسَبُ الإِنسَانُ أَلَّن نَجْمَعَ عِظَامَهُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 3
Sin, mutum yana zaton cẽwa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba?
بَلَى قَادِرِينَ عَلَى أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 4
Na'am! Mãsu ĩkon yi Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa.
بَلْ يُرِيدُ الإِنسَانُ لِيَفْجُرَ أَمَامَهُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 5
Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa.
يَسْأَلُ أَيَّانَ يَوْمُ الْقِيَامَةِSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 6
Yanã tambaya: "Yaushe ne Rãnar ¡iyãma?"
فَإِذَا بَرِقَ الْبَصَرُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 7
To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli).
وَخَسَفَ الْقَمَرُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 8
Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).
وَجُمِعَ الشَّمْسُ وَالْقَمَرُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 9
Aka tãra rãnã da watã
يَقُولُ الإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ أَيْنَ الْمَفَرُّSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 10
Mutum zai ce a rãn nan "Ina wurin gudu?"
كَلاَّ لا وَزَرَSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 11
A'aha! bãbu mafaka.
إِلَى رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمُسْتَقَرُّSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 12
zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake.
يُنَبَّأُ الإِنسَانُ يَوْمَئِذٍ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 13
Ana gayã wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gabatar da wanda ya jinkirtar.
بَلِ الإِنسَانُ عَلَى نَفْسِهِ بَصِيرَةٌSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 14
Ba haka ba! Mutum, ga abin da ya shafi kansa, masani ne.
وَلَوْ أَلْقَى مَعَاذِيرَهُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 15
Kuma ko da yã jẽfa uzurorinsa (bã zã a saurãre shi ba).
لا تُحَرِّكْ بِهِ لِسَانَكَ لِتَعْجَلَ بِهِSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 16
Kada ka mõtsar da harshenka game da shi dõmin ka yi gaugãwar riƙe shi (Alƙur'ãni).
إِنَّ عَلَيْنَا جَمْعَهُ وَقُرْآنَهُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 17
Lalle ne, wãjibi ne a gare Mu, Mu tãra shi. Mu (tsare maka) karãtunsa.
فَإِذَا قَرَأْنَاهُ فَاتَّبِعْ قُرْآنَهُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 18
To idan Muka karanta shi sai ka bi karatunsa.
ثُمَّ إِنَّ عَلَيْنَا بَيَانَهُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 19
sa'an nan, lalle wãjibi ne a gare Mu, bayãninsa.
كَلاَّ بَلْ تُحِبُّونَ الْعَاجِلَةَSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 20
A'aha! Bã haka ba kunã son mai gaugawar nan (duniya) ne.
وَتَذَرُونَ الآخِرَةَSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 21
Kunã barin ta ƙarshen (Lãhira).
وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاضِرَةٌSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 22
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu annuri ne.
إِلَى رَبِّهَا نَاظِرَةٌSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 23
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu kallo ne.
وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ بَاسِرَةٌSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 24
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu gintsẽwa ne.
تَظُنُّ أَن يُفْعَلَ بِهَا فَاقِرَةٌSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 25
Sunã zaton a sako musu masĩfa mai karya tsatso.
كَلاَّ إِذَا بَلَغَتْ التَّرَاقِيَSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 26
A'aha! Iadan (rai) ya kai ga karankarmai.
وَقِيلَ مَنْ رَاقٍSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 27
kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"
وَظَنَّ أَنَّهُ الْفِرَاقُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 28
Kuma ya tabbata cẽwa rabuwa dai ce.
وَالْتَفَّتِ السَّاقُ بِالسَّاقِSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 29
Kuma ƙwabri ya lauye da wani ƙwabri.
إِلَى رَبِّكَ يَوْمَئِذٍ الْمَسَاقُSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 30
Zuwa ga Ubangijinka, a rãnar nan, magargaɗa take.
فَلا صَدَّقَ وَلا صَلَّىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 31
To, bai gaskatã ba, kuma bai yi salla ba!
وَلَكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 32
Amma dai ya ƙaryata, kuma ya jũya baya!
ثُمَّ ذَهَبَ إِلَى أَهْلِهِ يَتَمَطَّىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 33
Sa'an nan, ya tafi zuwa ga mutãnensa, yana tãƙama.
أَوْلَى لَكَ فَأَوْلَىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 34
Halaka tã tabbata a gare ka, sa'an nan ita ce mafi dãcewa.
ثُمَّ أَوْلَى لَكَ فَأَوْلَىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 35
Sa'an nan, wata halaka tã tabbata a gare ka dõmin tã fi dãce wa.
أَيَحْسَبُ الإِنسَانُ أَن يُتْرَكَ سُدًىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 36
Shin, mutum nã zaton a bar shi sagaga (wãto bãbu nufin kõme game da shi)?
أَلَمْ يَكُ نُطْفَةً مِّن مَّنِيٍّ يُمْنَىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 37
Bai kasance iɗgo na maniyyi ba, wanda ake jefarwa (a cikin mahaifa)
ثُمَّ كَانَ عَلَقَةً فَخَلَقَ فَسَوَّىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 38
Sa'an nan, ya zama gudan jini, sa'an nan Allah Ya halitta shi, sa'an nan Ya daidaita gaɓõɓinsa;
فَجَعَلَ مِنْهُ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالأُنثَىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 39
Sa'an nan, Ya sanya daga gare shi, nau'i biyu: namiji damace?
أَلَيْسَ ذَلِكَ بِقَادِرٍ عَلَى أَن يُحْيِيَ الْمَوْتَىSorah Al-Qiyamah ( The Resurrection ) Verse Number 40
Ashẽ wannan bai zama Mai iko ba bisa ga rãyar da matattu?