Hausa
Sorah Nooh

Verses Number 28

إِنَّا أَرْسَلْنَا نُوحًا إِلَى قَوْمِهِ أَنْ أَنذِرْ قَوْمَكَ مِن قَبْلِ أَن يَأْتِيَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌSorah Nooh Verse Number 1
Lalle ne Mun aiki Nũhu zuwa ga mutãnensa, cẽwa ka yi gargaɗi ga mutãnenka gabãnin wata azãba mai raɗaɗi ta zo musu.
قَالَ يَا قَوْمِ إِنِّي لَكُمْ نَذِيرٌ مُّبِينٌSorah Nooh Verse Number 2
Ya ce: "Ya mutãnena ni, a gare ku, mai gargaɗi ne, mai bayyanãwa."
أَنِ اعْبُدُوا اللَّهَ وَاتَّقُوهُ وَأَطِيعُونِSorah Nooh Verse Number 3
"Cewa ku bauta wa Allah, ku ji tsõronSa, kuma ku bĩ ni."
يَغْفِرْ لَكُم مِّن ذُنُوبِكُمْ وَيُؤَخِّرْكُمْ إِلَى أَجَلٍ مُّسَمًّى إِنَّ أَجَلَ اللَّهِ إِذَا جَاءَ لا يُؤَخَّرُ لَوْ كُنتُمْ تَعْلَمُونَSorah Nooh Verse Number 4
"Allah zai gãfarta muku daga zunubanku kuma Ya jinkirta muku zuwa ga ajalin da aka ambata. Lalle ne ajalin Allah idan ya zo, ba za a jinkirta Shi ba, dã kun kasance masana (ga abin da nake faɗã dã, kun bar kãfirci)."
قَالَ رَبِّ إِنِّي دَعَوْتُ قَوْمِي لَيْلا وَنَهَارًاSorah Nooh Verse Number 5
Nũhu) ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne, na kirãyi mutãnena, a cikin dare da yini."
فَلَمْ يَزِدْهُمْ دُعَائِي إِلاَّ فِرَارًاSorah Nooh Verse Number 6
"To, amma kirana bai ƙãre su ba sai da, gudu (daga gare ni)."
وَإِنِّي كُلَّمَا دَعَوْتُهُمْ لِتَغْفِرَ لَهُمْ جَعَلُوا أَصَابِعَهُمْ فِي آذَانِهِمْ وَاسْتَغْشَوْا ثِيَابَهُمْ وَأَصَرُّوا وَاسْتَكْبَرُوا اسْتِكْبَارًاSorah Nooh Verse Number 7
"Kuma lalle ne ni, kõ da yaushe na kirãye su dõmin Ka gãfarta musu, sai su sanya yatsunsu a cikin kunnuwansu, su lulluɓe da tufãfinsu, su dõge ga yin laifi. Sun yi girman kai iyãkar girman kai."
ثُمَّ إِنِّي دَعَوْتُهُمْ جِهَارًاSorah Nooh Verse Number 8
"Sa'an nan lalle ne ni, na kira su, a bayyane."
ثُمَّ إِنِّي أَعْلَنتُ لَهُمْ وَأَسْرَرْتُ لَهُمْ إِسْرَارًاSorah Nooh Verse Number 9
"Sa'an nan lalle ne, na yi yẽkuwa sabõda su, kuma na gãna da su a cikin asĩri."
فَقُلْتُ اسْتَغْفِرُوا رَبَّكُمْ إِنَّهُ كَانَ غَفَّارًاSorah Nooh Verse Number 10
"Shi na ce, 'Ku nẽmi gãfara daga Ubangijinku, lalle ne shi Ya kasance Mai gãfara ne."
يُرْسِلِ السَّمَاء عَلَيْكُم مِّدْرَارًاSorah Nooh Verse Number 11
"Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ɓuɓɓuga."
وَيُمْدِدْكُمْ بِأَمْوَالٍ وَبَنِينَ وَيَجْعَل لَّكُمْ جَنَّاتٍ وَيَجْعَل لَّكُمْ أَنْهَارًاSorah Nooh Verse Number 12
"Kuma ya yalwata muku game da dũkiya da ɗiya, Ya sanya muku (albarka) ga gõnaki, kuma Ya sanya muku koguna."
مَّا لَكُمْ لا تَرْجُونَ لِلَّهِ وَقَارًاSorah Nooh Verse Number 13
"Me ya sãme ku, bã ku fãtar sãmun natsuwa daga Allah,"
وَقَدْ خَلَقَكُمْ أَطْوَارًاSorah Nooh Verse Number 14
"Alhãli kuwa, lalle ne, Ya halitta. ku, a cikin hãlãye?"
أَلَمْ تَرَوْا كَيْفَ خَلَقَ اللَّهُ سَبْعَ سَمَاوَاتٍ طِبَاقًاSorah Nooh Verse Number 15
"Ba ku ga yadda Allah Ya halitta wasu sammai bakwai ɗabaƙõƙĩ a kan jũna ba?"
وَجَعَلَ الْقَمَرَ فِيهِنَّ نُورًا وَجَعَلَ الشَّمْسَ سِرَاجًاSorah Nooh Verse Number 16
"Ya sanya watã a cikinsu, yana mai haske, Ya sanya rãnã babbar fitila?"
وَاللَّهُ أَنبَتَكُم مِّنَ الأَرْضِ نَبَاتًاSorah Nooh Verse Number 17
"Kuma Allah Ya tsirar da ku daga ƙasa (kamar ganye) tsirarwa."
ثُمَّ يُعِيدُكُمْ فِيهَا وَيُخْرِجُكُمْ إِخْرَاجًاSorah Nooh Verse Number 18
"Sa'an nan Ya mayar da ku a cikinta, kuma Ya fitar da ku fitarwa."
وَاللَّهُ جَعَلَ لَكُمُ الأَرْضَ بِسَاطًاSorah Nooh Verse Number 19
"Kuma Allah Ya sanya muku ƙasa shimfidaɗɗiya."
لِتَسْلُكُوا مِنْهَا سُبُلا فِجَاجًاSorah Nooh Verse Number 20
"Dõmin ku shiga a cikinta, hanyõyi mãsu fãɗi."
قَالَ نُوحٌ رَّبِّ إِنَّهُمْ عَصَوْنِي وَاتَّبَعُوا مَن لَّمْ يَزِدْهُ مَالُهُ وَوَلَدُهُ إِلاَّ خَسَارًاSorah Nooh Verse Number 21
Nũhu ya ce: "Ya Ubangijina! Lalle ne sũ sun saɓa mini sun bi wanda dukiyarsa da ɗiyansa ba su ƙãre shi da kõme ba sai da hasãra."
وَمَكَرُوا مَكْرًا كُبَّارًاSorah Nooh Verse Number 22
"Kuma sun yi wani mãkirci, mãkirci babba."
وَقَالُوا لا تَذَرُنَّ آلِهَتَكُمْ وَلا تَذَرُنَّ وَدًّا وَلا سُوَاعًا وَلا يَغُوثَ وَيَعُوقَ وَنَسْرًاSorah Nooh Verse Number 23
"Kuma suka ce: Faufau kada ku bar gumãkanku, kuma faufau, kada ku bar wadda, kuma kada ku bar suwã kuma kada ku bar Yagũsa da Ya'ũƙa da Nasra."
وَقَدْ أَضَلُّوا كَثِيرًا وَلا تَزِدِ الظَّالِمِينَ إِلاَّ ضَلالاSorah Nooh Verse Number 24
"Kuma lalle ne sun ɓatar da (mutãne) mãsu yawa, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai (kõme) sai ɓata."
مِمَّا خَطِيئَاتِهِمْ أُغْرِقُوا فَأُدْخِلُوا نَارًا فَلَمْ يَجِدُوا لَهُم مِّن دُونِ اللَّهِ أَنصَارًاSorah Nooh Verse Number 25
Sabõda laifukansu na ganganci aka nutsar da su, sa'an nan aka sanya su a wuta. Saboda haka ba su sãmã wa kansu wani mataimaki wanin Allah ba.
وَقَالَ نُوحٌ رَّبِّ لا تَذَرْ عَلَى الأَرْضِ مِنَ الْكَافِرِينَ دَيَّارًاSorah Nooh Verse Number 26
Kuma Nũhu ya ce: "Ya Ublngijina! Kada Ka bari, a kan ƙasa, daga cikin kãfirai, wanda ke zama a cikin gida."
إِنَّكَ إِن تَذَرْهُمْ يُضِلُّوا عِبَادَكَ وَلا يَلِدُوا إِلاَّ فَاجِرًا كَفَّارًاSorah Nooh Verse Number 27
"Lalle ne, Kai idan Ka bar su, zã su ɓatar da bãyinKa, kuma bã zã su haifi kowa ba fãce fãjiri mai yawan kãfirci"
رَبِّ اغْفِرْ لِي وَلِوَالِدَيَّ وَلِمَن دَخَلَ بَيْتِيَ مُؤْمِنًا وَلِلْمُؤْمِنِينَ وَالْمُؤْمِنَاتِ وَلا تَزِدِ الظَّالِمِينَ إِلاَّ تَبَارًاSorah Nooh Verse Number 28
"Ya Ubanginjina! Ka yi mini gãfara (ni) da mahaifana biyu, da wanda ya shiga gidana, yana mai ĩmãni, da mũminai maza da mũminai mãtã, kuma kada Ka ƙãrã wa azzãlumai kõme sai halaka."