Hausa
Sorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent )

Verses Number 44

سَأَلَ سَائِلٌ بِعَذَابٍ وَاقِعٍSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 1
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.
لِّلْكَافِرِينَ لَيْسَ لَهُ دَافِعٌSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 2
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.
مِّنَ اللَّهِ ذِي الْمَعَارِجِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 3
Daga Allah Mai matãkala.
تَعْرُجُ الْمَلائِكَةُ وَالرُّوحُ إِلَيْهِ فِي يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 4
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.
فَاصْبِرْ صَبْرًا جَمِيلاSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 5
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.
إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُ بَعِيدًاSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 6
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.
وَنَرَاهُ قَرِيبًاSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 7
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.
يَوْمَ تَكُونُ السَّمَاء كَالْمُهْلِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 8
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.
وَتَكُونُ الْجِبَالُ كَالْعِهْنِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 9
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.
وَلا يَسْأَلُ حَمِيمٌ حَمِيمًاSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 10
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.
يُبَصَّرُونَهُمْ يَوَدُّ الْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِي مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍ بِبَنِيهِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 11
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
وَصَاحِبَتِهِ وَأَخِيهِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 12
Da matarsa da ɗan'uwansa.
وَفَصِيلَتِهِ الَّتِي تُؤْويهِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 13
Da danginsa, mãsu tattarã shi.
وَمَن فِي الأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 14
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
كَلاَّ إِنَّهَا لَظَىSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 15
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
نَزَّاعَةً لِّلشَّوَىSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 16
Mai twãle fãtar goshi.
تَدْعُو مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 17
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
وَجَمَعَ فَأَوْعَىSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 18
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
إِنَّ الإِنسَانَ خُلِقَ هَلُوعًاSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 19
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
إِذَا مَسَّهُ الشَّرُّ جَزُوعًاSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 20
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
وَإِذَا مَسَّهُ الْخَيْرُ مَنُوعًاSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 21
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
إِلاَّ الْمُصَلِّينَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 22
Sai mãsu yin salla,
الَّذِينَ هُمْ عَلَى صَلاتِهِمْ دَائِمُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 23
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
وَالَّذِينَ فِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 24
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 25
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
وَالَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ الدِّينِSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 26
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
وَالَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 27
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 28
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
وَالَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَافِظُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 29
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
إِلاَّ عَلَى أَزْوَاجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَانُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 30
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
فَمَنِ ابْتَغَى وَرَاء ذَلِكَ فَأُولَئِكَ هُمُ الْعَادُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 31
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
وَالَّذِينَ هُمْ لِأَمَانَاتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَاعُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 32
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
وَالَّذِينَ هُم بِشَهَادَاتِهِمْ قَائِمُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 33
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
وَالَّذِينَ هُمْ عَلَى صَلاتِهِمْ يُحَافِظُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 34
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
أُوْلَئِكَ فِي جَنَّاتٍ مُّكْرَمُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 35
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
فَمَالِ الَّذِينَ كَفَرُوا قِبَلَكَ مُهْطِعِينَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 36
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
عَنِ الْيَمِينِ وَعَنِ الشِّمَالِ عِزِينَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 37
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
أَيَطْمَعُ كُلُّ امْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 38
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
كَلاَّ إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 39
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.
فَلا أُقْسِمُ بِرَبِّ الْمَشَارِقِ وَالْمَغَارِبِ إِنَّا لَقَادِرُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 40
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.
عَلَى أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 41
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.
فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا وَيَلْعَبُوا حَتَّى يُلاقُوا يَوْمَهُمُ الَّذِي يُوعَدُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 42
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).
يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ الأَجْدَاثِ سِرَاعًا كَأَنَّهُمْ إِلَى نُصُبٍ يُوفِضُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 43
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.
خَاشِعَةً أَبْصَارُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ذَلِكَ الْيَوْمُ الَّذِي كَانُوا يُوعَدُونَSorah Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) Verse Number 44
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)