Hausa
Sorah Al-Haaqqah ( The Inevitable )

Verses Number 52

الْحَاقَّةُSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 1
Kiran gaskiya!
مَا الْحَاقَّةُSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 2
Mẽne ne kiran gaskiya?
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحَاقَّةُSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 3
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌ بِالْقَارِعَةِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 4
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا بِالطَّاغِيَةِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 5
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 6
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَانِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى الْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَى كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 7
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
فَهَلْ تَرَى لَهُم مِّن بَاقِيَةٍSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 8
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?
وَجَاءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُ وَالْمُؤْتَفِكَاتُ بِالْخَاطِئَةِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 9
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
فَعَصَوْا رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةًSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 10
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
إِنَّا لَمَّا طَغَى الْمَاء حَمَلْنَاكُمْ فِي الْجَارِيَةِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 11
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَا أُذُنٌ وَاعِيَةٌSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 12
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
فَإِذَا نُفِخَ فِي الصُّورِ نَفْخَةٌ وَاحِدَةٌSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 13
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
وَحُمِلَتِ الأَرْضُ وَالْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَاحِدَةًSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 14
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ الْوَاقِعَةُSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 15
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
وَانشَقَّتِ السَّمَاء فَهِيَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 16
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
وَالْمَلَكُ عَلَى أَرْجَائِهَا وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَانِيَةٌSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 17
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لا تَخْفَى مِنكُمْ خَافِيَةٌSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 18
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ فَيَقُولُ هَاؤُمُ اقْرَؤُوا كِتَابِيَهْSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 19
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلاقٍ حِسَابِيَهْSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 20
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 21
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٍSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 22
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
قُطُوفُهَا دَانِيَةٌSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 23
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
كُلُوا وَاشْرَبُوا هَنِيئًا بِمَا أَسْلَفْتُمْ فِي الأَيَّامِ الْخَالِيَةِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 24
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِشِمَالِهِ فَيَقُولُ يَا لَيْتَنِي لَمْ أُوتَ كِتَابِيَهْSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 25
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 26
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
يَا لَيْتَهَا كَانَتِ الْقَاضِيَةَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 27
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
مَا أَغْنَى عَنِّي مَالِيَهْSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 28
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
هَلَكَ عَنِّي سُلْطَانِيَهْSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 29
"Ĩkona ya ɓace mini!"
خُذُوهُ فَغُلُّوهُSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 30
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
ثُمَّ الْجَحِيمَ صَلُّوهُSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 31
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
ثُمَّ فِي سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَاسْلُكُوهُSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 32
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
إِنَّهُ كَانَ لا يُؤْمِنُ بِاللَّهِ الْعَظِيمِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 33
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
وَلا يَحُضُّ عَلَى طَعَامِ الْمِسْكِينِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 34
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"
فَلَيْسَ لَهُ الْيَوْمَ هَاهُنَا حَمِيمٌSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 35
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
وَلا طَعَامٌ إِلاَّ مِنْ غِسْلِينٍSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 36
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
لا يَأْكُلُهُ إِلاَّ الْخَاطِؤُونَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 37
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
فَلا أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 38
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
وَمَا لا تُبْصِرُونَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 39
Da abin da bã ku iya gani.
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 40
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ قَلِيلا مَا تُؤْمِنُونَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 41
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
وَلا بِقَوْلِ كَاهِنٍ قَلِيلا مَا تَذَكَّرُونَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 42
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ الْعَالَمِينَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 43
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ الأَقَاوِيلِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 44
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِالْيَمِينِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 45
Dã Mun kãma shi da dãma.
ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ الْوَتِينَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 46
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَاجِزِينَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 47
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.
وَإِنَّهُ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 48
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 49
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
وَإِنَّهُ لَحَسْرَةٌ عَلَى الْكَافِرِينَSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 50
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
وَإِنَّهُ لَحَقُّ الْيَقِينِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 51
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.
فَسَبِّحْ بِاسْمِ رَبِّكَ الْعَظِيمِSorah Al-Haaqqah ( The Inevitable ) Verse Number 52
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.