Hausa
Sorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse )

Verses Number 78

الرَّحْمَنُSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 1
(Allah) Mai rahama.
عَلَّمَ الْقُرْآنَSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 2
Yã sanar da Alƙur'ani.
خَلَقَ الإِنسَانَSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 3
Yã halitta mutum.
عَلَّمَهُ الْبَيَانَSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 4
Yã sanar da shi bayãni (magana).
الشَّمْسُ وَالْقَمَرُ بِحُسْبَانٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 5
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
وَالنَّجْمُ وَالشَّجَرُ يَسْجُدَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 6
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
وَالسَّمَاءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ الْمِيزَانَSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 7
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
أَلاَّ تَطْغَوْا فِي الْمِيزَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 8
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
وَأَقِيمُوا الْوَزْنَ بِالْقِسْطِ وَلا تُخْسِرُوا الْمِيزَانَSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 9
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
وَالأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 10
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
فِيهَا فَاكِهَةٌ وَالنَّخْلُ ذَاتُ الأَكْمَامِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 11
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
وَالْحَبُّ ذُو الْعَصْفِ وَالرَّيْحَانُSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 12
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 13
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?
خَلَقَ الإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ كَالْفَخَّارِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 14
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
وَخَلَقَ الْجَانَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 15
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 16
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
رَبُّ الْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ الْمَغْرِبَيْنِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 17
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 18
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مَرَجَ الْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 19
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لّا يَبْغِيَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 20
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 21
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَخْرُجُ مِنْهُمَا اللُّؤْلُؤُ وَالْمَرْجَانُSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 22
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 23
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَلَهُ الْجَوَارِ الْمُنشَآتُ فِي الْبَحْرِ كَالأَعْلامِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 24
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 25
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 26
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.
وَيَبْقَى وَجْهُ رَبِّكَ ذُو الْجَلاَلِ وَالإِكْرَامِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 27
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 28
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَسْأَلُهُ مَن فِي السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِي شَأْنٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 29
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 30
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ الثَّقَلانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 31
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 32
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يَا مَعْشَرَ الْجِنِّ وَالإِنسِ إِنِ اسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا مِنْ أَقْطَارِ السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ فَانفُذُوا لا تَنفُذُونَ إِلاَّ بِسُلْطَانٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 33
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 34
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلا تَنتَصِرَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 35
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 36
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فَإِذَا انشَقَّتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَالدِّهَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 37
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 38
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فَيَوْمَئِذٍ لّا يُسْأَلُ عَن ذَنبِهِ إِنسٌ وَلا جَانٌّSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 39
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 40
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
يُعْرَفُ الْمُجْرِمُونَ بِسِيمَاهُمْ فَيُؤْخَذُ بِالنَّوَاصِي وَالأَقْدَامِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 41
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 42
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
هَذِهِ جَهَنَّمُ الَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا الْمُجْرِمُونَSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 43
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.
يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ آنٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 44
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 45
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِ جَنَّتَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 46
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 47
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
ذَوَاتَا أَفْنَانٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 48
Mãsu rassan itãce.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 49
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 50
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 51
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا مِن كُلِّ فَاكِهَةٍ زَوْجَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 52
A cikinsu akwai nau'i biyu daga kõwane 'ya'yan itãcen marmari.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 53
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُتَّكِئِينَ عَلَى فُرُشٍ بَطَائِنُهَا مِنْ إِسْتَبْرَقٍ وَجَنَى الْجَنَّتَيْنِ دَانٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 54
Sunã gincire a kan waɗansu shimfiɗu cikinsu tufãfin alharĩni mai kauri ne kuma nũnannun 'yã'yan itãcen Aljannar biyu kusakusa suke.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 55
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِنَّ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلا جَانٌّSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 56
A cikinsu akwai mãtã mãsu taƙaita ganinsu, wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗebe budurcinsu ba kuma haka wani aljani.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 57
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
كَأَنَّهُنَّ الْيَاقُوتُ وَالْمَرْجَانُSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 58
Kamar dai su yaƙũtu ne da murjãni.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 59
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
هَلْ جَزَاءُ الإِحْسَانِ إِلاَّ الإِحْسَانُSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 60
Shin, kyautatãwa nã da wani sakamako? (Ã'aha) fãce kyautatãwa.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 61
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 62
Kuma baicinsu akwai waɗansu gidãjen Aljanna biyu.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 63
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُدْهَامَّتَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 64
Mãsu duhun inuwa.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 65
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا عَيْنَانِ نَضَّاخَتَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 66
A cikinsu akwai marẽmari biyu masu kwarãrar ruwa.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 67
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِمَا فَاكِهَةٌ وَنَخْلٌ وَرُمَّانٌSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 68
A cikinsu akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno darummãni.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 69
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
فِيهِنَّ خَيْرَاتٌ حِسَانٌSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 70
A cikinsu, akwai wasu mãtã mãsu kyaun hãlãye, mãsu kyaun halitta.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 71
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
حُورٌ مَّقْصُورَاتٌ فِي الْخِيَامِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 72
Mãsu farin idãnu da baƙinsu waɗanda aka tsare a cikin haimõmi.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 73
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
لَمْ يَطْمِثْهُنَّ إِنسٌ قَبْلَهُمْ وَلا جَانٌّSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 74
Wani mutum, gabanin mazajensu bai ɗẽbe budurcinsu ba, kuma haka wani aljani.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 75
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
مُتَّكِئِينَ عَلَى رَفْرَفٍ خُضْرٍ وَعَبْقَرِيٍّ حِسَانٍSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 76
Sunã gincire a kan wasu matãsai mãsu kõren launi da katĩfun Abkara kyãwãwa.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 77
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
تَبَارَكَ اسْمُ رَبِّكَ ذِي الْجَلالِ وَالإِكْرَامِSorah Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) Verse Number 78
Sũnan Ubangjinka, Mai girman Jalãla da Karimci, ya tsarkaka.