Hausa
Sorah Al-Qamar ( The Moon )

Verses Number 55

اقْتَرَبَتِ السَّاعَةُ وَانشَقَّ الْقَمَرُSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 1
Sã'a ta yi kusa, kuma wata ya tsãge.
وَإِن يَرَوْا آيَةً يُعْرِضُوا وَيَقُولُوا سِحْرٌ مُّسْتَمِرٌّSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 2
Kuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"
وَكَذَّبُوا وَاتَّبَعُوا أَهْوَاءَهُمْ وَكُلُّ أَمْرٍ مُّسْتَقِرٌّSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 3
Kuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.
وَلَقَدْ جَاءَهُم مِّنَ الأَنبَاء مَا فِيهِ مُزْدَجَرٌSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 4
Kuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.
حِكْمَةٌ بَالِغَةٌ فَمَا تُغْنِ النُّذُرُSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 5
Hikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ يَوْمَ يَدْعُ الدَّاعِ إِلَى شَيْءٍ نُّكُرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 6
Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.
خُشَّعًا أَبْصَارُهُمْ يَخْرُجُونَ مِنَ الأَجْدَاثِ كَأَنَّهُمْ جَرَادٌ مُّنتَشِرٌSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 7
¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.
مُّهْطِعِينَ إِلَى الدَّاعِ يَقُولُ الْكَافِرُونَ هَذَا يَوْمٌ عَسِرٌSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 8
Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"
كَذَّبَتْ قَبْلَهُمْ قَوْمُ نُوحٍ فَكَذَّبُوا عَبْدَنَا وَقَالُوا مَجْنُونٌ وَازْدُجِرَSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 9
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata BawanMu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.
فَدَعَا رَبَّهُ أَنِّي مَغْلُوبٌ فَانتَصِرْSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 10
Sabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."
فَفَتَحْنَا أَبْوَابَ السَّمَاءِ بِمَاء مُّنْهَمِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 11
Sai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.
وَفَجَّرْنَا الأَرْضَ عُيُونًا فَالْتَقَى الْمَاءُ عَلَى أَمْرٍ قَدْ قُدِرَSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 12
Kuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umurni da aka riga aka ƙaddara shi.
وَحَمَلْنَاهُ عَلَى ذَاتِ أَلْوَاحٍ وَدُسُرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 13
Kuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.
تَجْرِي بِأَعْيُنِنَا جَزَاءً لِّمَن كَانَ كُفِرَSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 14
Tanã gudãna, a kan idãnunMu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.
وَلَقَد تَّرَكْنَاهَا آيَةً فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 15
Kuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 16
To, yãyã azãbãTa take da gargaɗiNa?
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 17
Kuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ عَادٌ فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 18
Ãdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗiNa?
إِنَّا أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ رِيحًا صَرْصَرًا فِي يَوْمِ نَحْسٍ مُّسْتَمِرٍّSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 19
Lalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.
تَنزِعُ النَّاسَ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ مُّنقَعِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 20
Tanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 21
To, yãya azãbãTa take da gargaɗiNa?
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 22
Kuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِالنُّذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 23
Samũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.
فَقَالُوا أَبَشَرًا مِّنَّا وَاحِدًا نَّتَّبِعُهُ إِنَّا إِذًا لَّفِي ضَلالٍ وَسُعُرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 24
Sai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.
أَءُلْقِيَ الذِّكْرُ عَلَيْهِ مِن بَيْنِنَا بَلْ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٌSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 25
"Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã'a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"
سَيَعْلَمُونَ غَدًا مَّنِ الْكَذَّابُ الأَشِرُSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 26
Zã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?
إِنَّا مُرْسِلُوا النَّاقَةِ فِتْنَةً لَّهُمْ فَارْتَقِبْهُمْ وَاصْطَبِرْSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 27
Lalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.
وَنَبِّئْهُمْ أَنَّ الْمَاءَ قِسْمَةٌ بَيْنَهُمْ كُلُّ شِرْبٍ مُّحْتَضَرٌSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 28
Kuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.
فَنَادَوْا صَاحِبَهُمْ فَتَعَاطَى فَعَقَرَSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 29
Sai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya sõke ta,
فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 30
To, yãya azãbaTa take da gargaɗiNa?
إِنَّا أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ صَيْحَةً وَاحِدَةً فَكَانُوا كَهَشِيمِ الْمُحْتَظِرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 31
Lalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 32
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ بِالنُّذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 33
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.
إِنَّا أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ حَاصِبًا إِلاَّ آلَ لُوطٍ نَّجَّيْنَاهُم بِسَحَرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 34
Lalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.
نِعْمَةً مِّنْ عِندِنَا كَذَلِكَ نَجْزِي مَن شَكَرَSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 35
Sabõda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.
وَلَقَدْ أَنذَرَهُم بَطْشَتَنَا فَتَمَارَوْا بِالنُّذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 36
Kuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙarMu, sai suka yi musu game da gargaɗin.
وَلَقَدْ رَاوَدُوهُ عَن ضَيْفِهِ فَطَمَسْنَا أَعْيُنَهُمْ فَذُوقُوا عَذَابِي وَنُذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 37
Kuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩNa."
وَلَقَدْ صَبَّحَهُم بُكْرَةً عَذَابٌ مُّسْتَقِرٌّSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 38
Kuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.
فَذُوقُوا عَذَابِي وَنُذُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 39
To, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩNa.
وَلَقَدْ يَسَّرْنَا الْقُرْآنَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 40
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?
وَلَقَدْ جَاءَ آلَ فِرْعَوْنَ النُّذُرُSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 41
Kuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir'auna.
كَذَّبُوا بِآيَاتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذْنَاهُمْ أَخْذَ عَزِيزٍ مُّقْتَدِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 42
Sun ƙaryata game da ãyõyinMu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.
أَكُفَّارُكُمْ خَيْرٌ مِّنْ أُوْلَئِكُمْ أَمْ لَكُم بَرَاءَةٌ فِي الزُّبُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 43
Shin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?
أَمْ يَقُولُونَ نَحْنُ جَمِيعٌ مُّنتَصِرٌSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 44
Kõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"
سَيُهْزَمُ الْجَمْعُ وَيُوَلُّونَ الدُّبُرَSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 45
Zã a karya tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.
بَلِ السَّاعَةُ مَوْعِدُهُمْ وَالسَّاعَةُ أَدْهَى وَأَمَرُّSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 46
Ã'a, Sã'a ita cẽ lõkacin wa'adinsu, kuma Sã'ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.
إِنَّ الْمُجْرِمِينَ فِي ضَلالٍ وَسُعُرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 47
Lalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.
يَوْمَ يُسْحَبُونَ فِي النَّارِ عَلَى وُجُوهِهِمْ ذُوقُوا مَسَّ سَقَرَSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 48
Rãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."
إِنَّا كُلَّ شَيْءٍ خَلَقْنَاهُ بِقَدَرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 49
Lalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.
وَمَا أَمْرُنَا إِلاَّ وَاحِدَةٌ كَلَمْحٍ بِالْبَصَرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 50
Kuma umurninMu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.
وَلَقَدْ أَهْلَكْنَا أَشْيَاعَكُمْ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 51
Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?
وَكُلُّ شَيْءٍ فَعَلُوهُ فِي الزُّبُرِSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 52
Kuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.
وَكُلُّ صَغِيرٍ وَكَبِيرٍ مُسْتَطَرٌSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 53
Kuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَنَهَرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 54
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.
فِي مَقْعَدِ صِدْقٍ عِندَ مَلِيكٍ مُّقْتَدِرٍSorah Al-Qamar ( The Moon ) Verse Number 55
A cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.