Hausa
Sorah An-Najm ( The Star )

Verses Number 62

وَالنَّجْمِ إِذَا هَوَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da taurãron, a lõkacin da ya faku.
مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمْ وَمَا غَوَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 2
Ma'abũcinku bai ɓata ba, kuma bai ƙẽtare haddi ba.
وَمَا يَنطِقُ عَنِ الْهَوَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 3
Kuma bã ya yin magana daga son zuciyarsa.
إِنْ هُوَ إِلاَّ وَحْيٌ يُوحَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 4
(Maganarsa) ba ta zamo ba, fãce wahayi ne da ake aikõwa.
عَلَّمَهُ شَدِيدُ الْقُوَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 5
(Malã'ika) mai tsananin ƙarfi ya sanar da shi.
ذُو مِرَّةٍ فَاسْتَوَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 6
Ma'abũcin ƙarfi da kwarjini, sa'an nan ya daidaita.
وَهُوَ بِالأُفُقِ الأَعْلَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 7
Alhãli kuwa yanã a sararin samã mafi aukaka.
ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 8
Sa'an nan ya kusanta, kuma ya matsa zurõwa.
فَكَانَ قَابَ قَوْسَيْنِ أَوْ أَدْنَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 9
Har ya kasance gwargwadon zirã'i biyu, kõ kuma abin da ya fi kusa.
فَأَوْحَى إِلَى عَبْدِهِ مَا أَوْحَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 10
Sa'an nan ya yi wahayi zuwa ga bãwan Allah (Muhammadu) da abin da ya faɗa (masa).
مَا كَذَبَ الْفُؤَادُ مَا رَأَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 11
Zũciyar (Annabi) bata ƙaryata abin da ya gani ba.
أَفَتُمَارُونَهُ عَلَى مَا يَرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 12
Shin, zã ku yi masa musu a kan abin da yake gani?
وَلَقَدْ رَآهُ نَزْلَةً أُخْرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 13
Kuma lalle ya gan shi, haƙĩƙatan, a wani lõkacin saukarsa.
عِندَ سِدْرَةِ الْمُنتَهَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 14
A wurin da magaryar tuƙẽwa take.
عِندَهَا جَنَّةُ الْمَأْوَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 15
A inda taken, nan Aljannar makoma take.
إِذْ يَغْشَى السِّدْرَةَ مَا يَغْشَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 16
Lõkacin da abin da yake rufe magaryar tuƙẽwa ya rufe ta.
مَا زَاغَ الْبَصَرُ وَمَا طَغَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 17
Ganinsa bai karkata ba, kuma bai ƙetare haddi ba.
لَقَدْ رَأَى مِنْ آيَاتِ رَبِّهِ الْكُبْرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 18
Lalle, tabbas, (Annabinku) ya ga waɗanda suka fi girma daga ãyõyin Ubangijinsa.
أَفَرَأَيْتُمُ اللاَّتَ وَالْعُزَّىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 19
Shin, kun ga Lãta da uzza?
وَمَنَاةَ الثَّالِثَةَ الأُخْرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 20
Da (wani gunki wai shi) Manãta, na ukunsu?
أَلَكُمُ الذَّكَرُ وَلَهُ الأُنثَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 21
Ashe, kũ ne da ɗa namiji Shĩ (Allah) kuma da ɗiya mace?
تِلْكَ إِذًا قِسْمَةٌ ضِيزَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 22
Wannan fa ya zama rabo naƙasasshe.
إِنْ هِيَ إِلاَّ أَسْمَاءٌ سَمَّيْتُمُوهَا أَنتُمْ وَآبَاؤُكُم مَّا أَنزَلَ اللَّهُ بِهَا مِن سُلْطَانٍ إِن يَتَّبِعُونَ إِلاَّ الظَّنَّ وَمَا تَهْوَى الأَنفُسُ وَلَقَدْ جَاءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ الْهُدَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 23
Waɗannan bã kõme ba ne fãce sũnãye, waɗanda kuka ambace su da su, kũ da uwãyenku. Allah bai saukar da wani dalĩli game da su ba. (Kãfirai) bã su biyar kõme fãce zato da abin da rãyukansu ke so, Alhãli kuwa shiriyar ta daga wajen Ubangijinsu, ta jẽ musu (sai suka bar ta suka kõma wa zaton).
أَمْ لِلإِنسَانِ مَا تَمَنَّىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 24
Ko (an fai cẽwa) mutum zai sãmi abin da yake gũri?
فَلِلَّهِ الآخِرَةُ وَالأُولَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 25
To, Lãhira da dũniya na Allah kawai ne (wanda ya nẽme su daga wani, yã yi kuskure).
وَكَم مِّن مَّلَكٍ فِي السَّمَاوَاتِ لا تُغْنِي شَفَاعَتُهُمْ شَيْئًا إِلاَّ مِن بَعْدِ أَن يَأْذَنَ اللَّهُ لِمَن يَشَاءُ وَيَرْضَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 26
Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.
إِنَّ الَّذِينَ لا يُؤْمِنُونَ بِالآخِرَةِ لَيُسَمُّونَ الْمَلائِكَةَ تَسْمِيَةَ الأُنثَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 27
Lalle waɗannan da bã su yin ĩmãni da Lãhira, haƙĩƙa sunã kiran malã'iku da sũnan mace.
وَمَا لَهُم بِهِ مِنْ عِلْمٍ إِن يَتَّبِعُونَ إِلاَّ الظَّنَّ وَإِنَّ الظَّنَّ لا يُغْنِي مِنَ الْحَقِّ شَيْئًاSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 28
Kuma bã su da wani ilmi game da shi, bã su bin kõme fãce zato alhãli kuwa lalle zato bã ya amfãnar da kõme daga gaskiya.
فَأَعْرِضْ عَن مَّن تَوَلَّى عَن ذِكْرِنَا وَلَمْ يُرِدْ إِلاَّ الْحَيَاةَ الدُّنْيَاSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 29
Sabõda haka sai ka kau da kai daga wanda ya jũya bãya daga ambatonMu kuma bai yi nufin kõme ba fãce rãyuwar kusa (dũniya).
ذَلِكَ مَبْلَغُهُم مِّنَ الْعِلْمِ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِ وَهُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اهْتَدَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 30
Wannan ita ce iyãkar abin da suke iya kai gare shi na ilmi. lalle Ubangijinka Shĩ ne Mafi sanin wanda ya ɓace daga hanyarSa, kuma Shi ne Mafi sani ga wanda ya nẽmi shiriya.
وَلِلَّهِ مَا فِي السَّمَاوَاتِ وَمَا فِي الأَرْضِ لِيَجْزِيَ الَّذِينَ أَسَاؤُوا بِمَا عَمِلُوا وَيَجْزِيَ الَّذِينَ أَحْسَنُوا بِالْحُسْنَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 31
Kuma abin da ke cikin sammai da abin da yake a cikin ƙasã na Allah kawai ne, dõmin Yã sãka wa waɗanda suka mũnana da abin da suka aikata, kuma Ya sãka wa waɗanda suki kyautata da sakamakon da ya fi kyau.
الَّذِينَ يَجْتَنِبُونَ كَبَائِرَ الإِثْمِ وَالْفَوَاحِشَ إِلاَّ اللَّمَمَ إِنَّ رَبَّكَ وَاسِعُ الْمَغْفِرَةِ هُوَ أَعْلَمُ بِكُمْ إِذْ أَنشَأَكُم مِّنَ الأَرْضِ وَإِذْ أَنتُمْ أَجِنَّةٌ فِي بُطُونِ أُمَّهَاتِكُمْ فَلا تُزَكُّوا أَنفُسَكُمْ هُوَ أَعْلَمُ بِمَنِ اتَّقَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 32
Waɗanda ke nĩsantar manyan zunubai da abũbuwan alfãsha, fãce ƙanãnan laifuffuka, lalle Ubangijinka Mai yalwatattar gãfara ne, Shĩ ne Ya fi sani ga abinda ke gare ku a lõkacin da Ya ƙãga halittarku daga ƙasa, kuma a lõkacin da kuke tãyuna a cikin cikannan uwãyenku. Sabõda haka, kada ku tsarkake kanku, Shĩ ne Mafi sani ga wanda ya yi taƙawa.
أَفَرَأَيْتَ الَّذِي تَوَلَّىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 33
Shin, ka ga wannan da ya jũya baya?
وَأَعْطَى قَلِيلاً وَأَكْدَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 34
Ya yi kyauta kaɗan, kuma ya yi rowa?
أَعِندَهُ عِلْمُ الْغَيْبِ فَهُوَ يَرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 35
Shin, akwai ilmin gaibi a wurinsa, Sabõda haka yanã ganin gaibin?
أَمْ لَمْ يُنَبَّأْ بِمَا فِي صُحُفِ مُوسَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 36
Ko kuwa ba a ba shi lãbãri ba ga abin da yake a cikin Littafan Mũsã?
وَإِبْرَاهِيمَ الَّذِي وَفَّىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 37
Da Ibrãhĩm wanda ya cika alkawari?
أَلاَّ تَزِرُ وَازِرَةٌ وِزْرَ أُخْرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 38
Cẽwa wani rai mai kãyan laifi bã ya ɗaukar kãyan laifin wani.
وَأَن لَّيْسَ لِلإِنسَانِ إِلاَّ مَا سَعَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 39
Kuma mutum bã shi da kõme fãce abin da ya aikata.
وَأَنَّ سَعْيَهُ سَوْفَ يُرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 40
Kuma lalle, aikinsa zã a gan shi.
ثُمَّ يُجْزَاهُ الْجَزَاءَ الأَوْفَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 41
Sa'an nan a sãka masa da sakamako wanda yake mafi cikar ma'auni?
وَأَنَّ إِلَى رَبِّكَ الْمُنتَهَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 42
Kuma lalle, makõmar zuwa Ubangijinka kawai take?
وَأَنَّهُ هُوَ أَضْحَكَ وَأَبْكَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 43
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya sanya dariya, kuma Ya sanya kũka.
وَأَنَّهُ هُوَ أَمَاتَ وَأَحْيَاSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 44
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya kashe, kuma Ya rãyar.
وَأَنَّهُ خَلَقَ الزَّوْجَيْنِ الذَّكَرَ وَالأُنثَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 45
Kuma lalle Shĩ ne Ya yi halitta nau'i-nau'i, namiji da mace.
مِن نُّطْفَةٍ إِذَا تُمْنَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 46
Daga wani ɗigon ruwa guda a lõkacin da ake jẽfa shi a cikin mahaifa.
وَأَنَّ عَلَيْهِ النَّشْأَةَ الأُخْرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 47
Kuma a kansa ne ƙãga halitta ta biyu take.
وَأَنَّهُ هُوَ أَغْنَى وَأَقْنَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 48
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya azurta, kuma Ya wadãtar.
وَأَنَّهُ هُوَ رَبُّ الشِّعْرَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 49
Kuma lalle, Shĩ, Shi ne Ubangijin Shi'ira.
وَأَنَّهُ أَهْلَكَ عَادًا الأُولَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 50
Kuma lalle, Shĩ, Shĩ ne Ya halaka Ãdãwa na farko.
وَثَمُودَ فَمَا أَبْقَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 51
Da Samũdãwa, sa'an nan bai rage su ba.
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ إِنَّهُمْ كَانُوا هُمْ أَظْلَمَ وَأَطْغَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 52
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sũ sun kasance mafi zãlunci kuma mafi girman kai.
وَالْمُؤْتَفِكَةَ أَهْوَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 53
Da waɗanda aka birkice ƙasarsu, Ya kãyar da su.
فَغَشَّاهَا مَا غَشَّىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 54
Sa'an nan abin da ya rufe su, ya rufe su.
فَبِأَيِّ آلاَءِ رَبِّكَ تَتَمَارَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 55
To, da wace daga ni'imõmin Ubangijinka kake yin shakka?
هَذَا نَذِيرٌ مِّنَ النُّذُرِ الأُولَىSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 56
wannan (Muhammadu) mai gargaɗi ne kamar irin mãsu gargaɗi na farko.
أَزِفَتِ الآزِفَةُSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 57
Makusanciya fa, tã yi kusa.
لَيْسَ لَهَا مِن دُونِ اللَّهِ كَاشِفَةٌSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 58
Bãbu wani rai, banda Allah, mai iya bãyani gare ta.
أَفَمِنْ هَذَا الْحَدِيثِ تَعْجَبُونَSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 59
Shin, kuma daga wannan lãbãri kuke mãmãki?
وَتَضْحَكُونَ وَلا تَبْكُونَSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 60
Kuma kunã yin dãriya, kuma bã ku yin kũka?
وَأَنتُمْ سَامِدُونَSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 61
Alhãli kunã mãsu wãsã?
فَاسْجُدُوا لِلَّهِ وَاعْبُدُواSorah An-Najm ( The Star ) Verse Number 62
To, ku yi tawãli'u ga Allah, kuma ku bauta (masa).