Hausa
Sorah At-Tur ( The Mount )

Verses Number 49

وَالطُّورِSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da ¦ũr (Dũtsen Mũsã).
وَكِتَابٍ مَّسْطُورٍSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 2
Da wani littãfi rubũtacce.
فِي رَقٍّ مَّنشُورٍSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 3
A cikin wata takardar fãta shimfiɗaɗɗa.
وَالْبَيْتِ الْمَعْمُورِSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 4
Da Gidan da aka rãyar da shi (da ibãda).
وَالسَّقْفِ الْمَرْفُوعِSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 5
Da rufin nan da aka ɗaukaka.
وَالْبَحْرِ الْمَسْجُورِSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 6
Da tẽkun nan da aka cika (da ruwa).
إِنَّ عَذَابَ رَبِّكَ لَوَاقِعٌSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 7
Lalle, azãbar Ubangijinka, haƙĩƙa, mai aukuwa ce.
مَا لَهُ مِن دَافِعٍSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 8
Bã ta da mai tunkuɗẽwa.
يَوْمَ تَمُورُ السَّمَاءُ مَوْرًاSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 9
Rãnar da samã ke yin mõtsi tanã kai kãwo.
وَتَسِيرُ الْجِبَالُ سَيْرًاSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 10
Kuma duwãtsu nã tafiya sunã shũɗẽwa.
فَوَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِلْمُكَذِّبِينَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 11
To, bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
الَّذِينَ هُمْ فِي خَوْضٍ يَلْعَبُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 12
Waɗanda suke a cikin kududdufi sunã wãsã.
يَوْمَ يُدَعُّونَ إِلَى نَارِ جَهَنَّمَ دَعًّاSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 13
Rãnar da zã a tunkuɗa su zuwa wutar Jahannama, tunkuɗãwa.
هَذِهِ النَّارُ الَّتِي كُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 14
(A ce musu): "Wannan ita ce wutar da kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
أَفَسِحْرٌ هَذَا أَمْ أَنتُمْ لا تُبْصِرُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 15
"To, shin wannan sihiri ne kõ kuwa kũ ne bã ku gani?"
اصْلَوْهَا فَاصْبِرُوا أَوْ لا تَصْبِرُوا سَوَاءٌ عَلَيْكُمْ إِنَّمَا تُجْزَوْنَ مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 16
"Ku shigẽ ta. To, ku yi haƙuri ko kuma kada ku yi haƙuri, dai dai ne a kanku, kawai anã yi muku sakamakon abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَنَعِيمٍSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 17
Lalle, mãsu taƙawa, sunã a cikin gidãjen Aljanna da wata ni'ima.
فَاكِهِينَ بِمَا آتَاهُمْ رَبُّهُمْ وَوَقَاهُمْ رَبُّهُمْ عَذَابَ الْجَحِيمِSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 18
Sunã mãsu jin dãɗi da abin da Ubangijinsu Ya ba su, kuma Ubangijinsu Ya tsãre musu azãbar Jahĩm.
كُلُوا وَاشْرَبُوا هَنِيئًا بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 19
(A ce musu): "Ku ci, ku sha, da ni'ima, dõmin abin da kuka kasance kunã aikatãwa."
مُتَّكِئِينَ عَلَى سُرُرٍ مَّصْفُوفَةٍ وَزَوَّجْنَاهُم بِحُورٍ عِينٍSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 20
Sunã kishingiɗe a kan karagu waɗanda ke cikin sahu, kuma Muka aurar da su waɗansu mãtã mãsu farin idãnu, mãsu girmansu.
وَالَّذِينَ آمَنُوا وَاتَّبَعَتْهُمْ ذُرِّيَّتُهُم بِإِيمَانٍ أَلْحَقْنَا بِهِمْ ذُرِّيَّتَهُمْ وَمَا أَلَتْنَاهُم مِّنْ عَمَلِهِم مِّن شَيْءٍ كُلُّ امْرِئٍ بِمَا كَسَبَ رَهِينٌSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 21
Kuma waɗanda suka yi ĩmãni kuma zũriyarsu suka bĩ su ga ĩmãnin, Mun riskar da zũriyarsu da su, alhãli kuwa bã da Mun rage musu kõme ba daga aikinsu, kõwane mutum jingina ne ga abin da ya sana'anta.
وَأَمْدَدْنَاهُم بِفَاكِهَةٍ وَلَحْمٍ مِّمَّا يَشْتَهُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 22
Kuma Muka yalwata musu 'ya'yan itãce da nãma irin wanda suke marmari.
يَتَنَازَعُونَ فِيهَا كَأْسًا لّا لَغْوٌ فِيهَا وَلا تَأْثِيمٌSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 23
Sunã mĩƙa wa jũnansu a cikinta hinjãlan giya, wadda bãbu yãsassar magana a cikinta, kuma bãbu jin nauyin zunubi.
وَيَطُوفُ عَلَيْهِمْ غِلْمَانٌ لَّهُمْ كَأَنَّهُمْ لُؤْلُؤٌ مَّكْنُونٌSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 24
Kuma waɗansu samãri nã gẽwayãwa a kansu, kamar dai sũ lu'ulu'u ne wanda ke kulle.
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَى بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 25
Waɗansunsu suka fuskanta zuwa ga waɗansu, sunã tambayar jũna.
قَالُوا إِنَّا كُنَّا قَبْلُ فِي أَهْلِنَا مُشْفِقِينَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 26
Suka ce: "Lalle mũ mun kasance a gabãnin wannan (a dũniya) a cikin iyãlanmu munã jin tsõro."
فَمَنَّ اللَّهُ عَلَيْنَا وَوَقَانَا عَذَابَ السَّمُومِSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 27
"To, Allah Yã yi mana kyautar falala, kuma Yã tsare mana azãbar iskar zãfi."
إِنَّا كُنَّا مِن قَبْلُ نَدْعُوهُ إِنَّهُ هُوَ الْبَرُّ الرَّحِيمُSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 28
"Lalle mũ mun kasance, a gãbanin haka, munã kiran sa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai kyautatãwa, Mai rahama."
فَذَكِّرْ فَمَا أَنتَ بِنِعْمَتِ رَبِّكَ بِكَاهِنٍ وَلا مَجْنُونٍSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 29
To, ka tunãtar kai fa sabõda ni'imar Ubangjinka, bã bõka kake ba, kuma bã mahaukaci ba.
أَمْ يَقُولُونَ شَاعِرٌ نَّتَرَبَّصُ بِهِ رَيْبَ الْمَنُونِSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 30
Shin zã su ce: "Mawãƙi ne, munã jiran, masĩfun mutuwa game da shĩ"?
قُلْ تَرَبَّصُوا فَإِنِّي مَعَكُم مِّنَ الْمُتَرَبِّصِينَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 31
Ka ce: "Ku yi jira, domin nĩ ma lalle inã a cikin mãsu jira tãre da ku."
أَمْ تَأْمُرُهُمْ أَحْلامُهُم بِهَذَا أَمْ هُمْ قَوْمٌ طَاغُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 32
Shin, hankulansu ne ke umarin su da wannan, kõ kuwa sũ wasu mutãne ne mãsu ƙetare haddi?
أَمْ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُ بَل لّا يُؤْمِنُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 33
Shin, cẽwa suke yi: "Shi ne ke ƙãga faɗarsa"? Ã'a ba su dai yi ĩmãni ba.
فَلْيَأْتُوا بِحَدِيثٍ مِّثْلِهِ إِن كَانُوا صَادِقِينَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 34
Sai su zõ da wani lãbãri mai misãlinsa idan sun kasance sũmãsu gaskiya ne.
أَمْ خُلِقُوا مِنْ غَيْرِ شَيْءٍ أَمْ هُمُ الْخَالِقُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 35
Shin, an halitta su ne bã daga kõme ba, kõ kuwa sũ ne mãsu yin halitta?
أَمْ خَلَقُوا السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضَ بَل لّا يُوقِنُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 36
Shin, sun halitta sammai da ƙasa ne? Ã'a ba su dai yi ĩmãnin yaƙĩni ba.
أَمْ عِندَهُمْ خَزَائِنُ رَبِّكَ أَمْ هُمُ الْمُصَيْطِرُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 37
Shin, taskõkin Ubangijinka, sunã a wurinsu ne? Kõ kuwa sũ ne mãsu rinjãya?
أَمْ لَهُمْ سُلَّمٌ يَسْتَمِعُونَ فِيهِ فَلْيَأْتِ مُسْتَمِعُهُم بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 38
Shin, sunã da wani tsãni ne wanda suke (hawa sunã) saurãron (lãbãrin samã) a cikinsa? Sai mai saurarõnsu ya zo da wani dalĩli bayyananne.
أَمْ لَهُ الْبَنَاتُ وَلَكُمُ الْبَنُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 39
Shin, Yanã da 'ya'ya mãtã ne kuma kũ, kunã da ɗiya maza ne?
أَمْ تَسْأَلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 40
Shin, kanã tambayar su wata ijãra ne, sabõda haka suka zama mãsu jin nauyin biyan tãrar?
أَمْ عِندَهُمُ الْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 41
Shin, a wurinsu akwai ilmin gaibi, sabõda haka sunã rubũtãwa?
أَمْ يُرِيدُونَ كَيْدًا فَالَّذِينَ كَفَرُوا هُمُ الْمَكِيدُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 42
Shin, sunã nufin wani kaidi ne? To, waɗanda suka kãfirta sũ ne waɗanda ake yi wa kaidi.
أَمْ لَهُمْ إِلَهٌ غَيْرُ اللَّهِ سُبْحَانَ اللَّهِ عَمَّا يُشْرِكُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 43
Shin, sunã da wani abin bautãwa ne wanda bã Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke yi na shirki!
وَإِن يَرَوْا كِسْفًا مِّنَ السَّمَاءِ سَاقِطًا يَقُولُوا سَحَابٌ مَّرْكُومٌSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 44
Kuma idan sun ga wani ɓaɓɓake daga samã yãnã fãɗuwa, sai su ce wani girgije ne, mai hauhawar jũna.
فَذَرْهُمْ حَتَّى يُلاقُوا يَوْمَهُمُ الَّذِي فِيهِ يُصْعَقُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 45
To, ka bar su, sai sun haɗu da yinin nan da za a sũmar da su a cikinsa.
يَوْمَ لا يُغْنِي عَنْهُمْ كَيْدُهُمْ شَيْئًا وَلا هُمْ يُنصَرُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 46
Rãnar da kaidinsu bã ya wadãtar masu da kõme, kuma bã a taimakon su.
وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا عَذَابًا دُونَ ذَلِكَ وَلَكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لا يَعْلَمُونَSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 47
Kuma lalle, waɗannan da suka yi zãluncin, sunã da azãba (a nan dũniya) banda waccan, kuma mafi yawansu ba su sani ba.
وَاصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعْيُنِنَا وَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 48
Sai ka yi hakuri da hukuncin Ubangijinka, lalle kai fa kanã idãnunMu, kuma ka tsarkake Ubangijinka da (tasbĩhi) game da gõde Masa a lõkacin da kake tãshi tsaye (dõmin salla kõ wani abu).
وَمِنَ اللَّيْلِ فَسَبِّحْهُ وَإِدْبَارَ النُّجُومِSorah At-Tur ( The Mount ) Verse Number 49
Kuma daga dare, sai ka tsarkake Shi (da tasbĩhin) dalõkacin jũyãwar taurãri.