Hausa
Sorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter )

Verses Number 60

وَالذَّارِيَاتِ ذَرْوًاSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
فَالْحَامِلاتِ وِقْرًاSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 2
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
فَالْجَارِيَاتِ يُسْرًاSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 3
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
فَالْمُقَسِّمَاتِ أَمْرًاSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 4
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٌSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 5
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
وَإِنَّ الدِّينَ لَوَاقِعٌSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 6
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الْحُبُكِSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 7
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
إِنَّكُمْ لَفِي قَوْلٍ مُّخْتَلِفٍSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 8
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
يُؤْفَكُ عَنْهُ مَنْ أُفِكَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 9
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
قُتِلَ الْخَرَّاصُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 10
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
الَّذِينَ هُمْ فِي غَمْرَةٍ سَاهُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 11
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
يَسْأَلُونَ أَيَّانَ يَوْمُ الدِّينِSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 12
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
يَوْمَ هُمْ عَلَى النَّارِ يُفْتَنُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 13
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
ذُوقُوا فِتْنَتَكُمْ هَذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تَسْتَعْجِلُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 14
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 15
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
آخِذِينَ مَا آتَاهُمْ رَبُّهُمْ إِنَّهُمْ كَانُوا قَبْلَ ذَلِكَ مُحْسِنِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 16
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
كَانُوا قَلِيلاً مِّنَ اللَّيْلِ مَا يَهْجَعُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 17
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
وَبِالأَسْحَارِ هُمْ يَسْتَغْفِرُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 18
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
وَفِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 19
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
وَفِي الأَرْضِ آيَاتٌ لِّلْمُوقِنِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 20
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
وَفِي أَنفُسِكُمْ أَفَلا تُبْصِرُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 21
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
وَفِي السَّمَاءِ رِزْقُكُمْ وَمَا تُوعَدُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 22
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
فَوَرَبِّ السَّمَاءِ وَالأَرْضِ إِنَّهُ لَحَقٌّ مِّثْلَ مَا أَنَّكُمْ تَنطِقُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 23
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ ضَيْفِ إِبْرَاهِيمَ الْمُكْرَمِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 24
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
إِذْ دَخَلُوا عَلَيْهِ فَقَالُوا سَلامًا قَالَ سَلامٌ قَوْمٌ مُّنكَرُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 25
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
فَرَاغَ إِلَى أَهْلِهِ فَجَاءَ بِعِجْلٍ سَمِينٍSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 26
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,
فَقَرَّبَهُ إِلَيْهِمْ قَالَ أَلا تَأْكُلُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 27
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
فَأَوْجَسَ مِنْهُمْ خِيفَةً قَالُوا لا تَخَفْ وَبَشَّرُوهُ بِغُلامٍ عَلِيمٍSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 28
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
فَأَقْبَلَتِ امْرَأَتُهُ فِي صَرَّةٍ فَصَكَّتْ وَجْهَهَا وَقَالَتْ عَجُوزٌ عَقِيمٌSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 29
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
قَالُوا كَذَلِكَ قَالَ رَبُّكِ إِنَّهُ هُوَ الْحَكِيمُ الْعَلِيمُSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 30
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا الْمُرْسَلُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 31
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"
قَالُوا إِنَّا أُرْسِلْنَا إِلَى قَوْمٍ مُّجْرِمِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 32
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن طِينٍSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 33
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
مُسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 34
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ الْمُؤْمِنِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 35
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍ مِّنَ الْمُسْلِمِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 36
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
وَتَرَكْنَا فِيهَا آيَةً لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ الْعَذَابَ الأَلِيمَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 37
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
وَفِي مُوسَى إِذْ أَرْسَلْنَاهُ إِلَى فِرْعَوْنَ بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 38
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.
فَتَوَلَّى بِرُكْنِهِ وَقَالَ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 39
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
فَأَخَذْنَاهُ وَجُنُودَهُ فَنَبَذْنَاهُمْ فِي الْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 40
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
وَفِي عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ الرِّيحَ الْعَقِيمَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 41
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
مَا تَذَرُ مِن شَيْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلاَّ جَعَلَتْهُ كَالرَّمِيمِSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 42
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
وَفِي ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا حَتَّى حِينٍSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 43
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
فَعَتَوْا عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ الصَّاعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 44
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
فَمَا اسْتَطَاعُوا مِن قِيَامٍ وَمَا كَانُوا مُنتَصِرِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 45
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ إِنَّهُمْ كَانُوا قَوْمًا فَاسِقِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 46
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
وَالسَّمَاءَ بَنَيْنَاهَا بِأَيْدٍ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 47
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
وَالأَرْضَ فَرَشْنَاهَا فَنِعْمَ الْمَاهِدُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 48
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
وَمِن كُلِّ شَيْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 49
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
فَفِرُّوا إِلَى اللَّهِ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 50
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
وَلا تَجْعَلُوا مَعَ اللَّهِ إِلَهًا آخَرَ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 51
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
كَذَلِكَ مَا أَتَى الَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلاَّ قَالُوا سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 52
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
أَتَوَاصَوْا بِهِ بَلْ هُمْ قَوْمٌ طَاغُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 53
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَا أَنتَ بِمَلُومٍSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 54
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
وَذَكِّرْ فَإِنَّ الذِّكْرَى تَنفَعُ الْمُؤْمِنِينَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 55
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالإِنسَ إِلاَّ لِيَعْبُدُونِSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 56
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
مَا أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍ وَمَا أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 57
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.
إِنَّ اللَّهَ هُوَ الرَّزَّاقُ ذُو الْقُوَّةِ الْمَتِينُSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 58
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا ذَنُوبًا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَابِهِمْ فَلا يَسْتَعْجِلُونِSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 59
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
فَوَيْلٌ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا مِن يَوْمِهِمُ الَّذِي يُوعَدُونَSorah Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) Verse Number 60
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.