Hausa
Sorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks )

Verses Number 182

وَالصَّافَّاتِ صَفًّاSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 1
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
فَالزَّاجِرَاتِ زَجْرًاSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 2
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
فَالتَّالِيَاتِ ذِكْرًاSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 3
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
إِنَّ إِلَهَكُمْ لَوَاحِدٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 4
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ الْمَشَارِقِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 5
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
إِنَّا زَيَّنَّا السَّمَاءَ الدُّنْيَا بِزِينَةٍ الْكَوَاكِبِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 6
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَانٍ مَّارِدٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 7
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
لا يَسَّمَّعُونَ إِلَى الْمَلإِ الأَعْلَى وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 8
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
دُحُورًا وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 9
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
إِلاَّ مَنْ خَطِفَ الْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ ثَاقِبٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 10
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
فَاسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَا إِنَّا خَلَقْنَاهُم مِّن طِينٍ لّازِبٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 11
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 12
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
وَإِذَا ذُكِّرُوا لا يَذْكُرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 13
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
وَإِذَا رَأَوْا آيَةً يَسْتَسْخِرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 14
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
وَقَالُوا إِنْ هَذَا إِلاَّ سِحْرٌ مُّبِينٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 15
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَئِنَّا لَمَبْعُوثُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 16
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
أَوَآبَاؤُنَا الأَوَّلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 17
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَاخِرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 18
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
فَإِنَّمَا هِيَ زَجْرَةٌ وَاحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 19
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
وَقَالُوا يَا وَيْلَنَا هَذَا يَوْمُ الدِّينِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 20
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
هَذَا يَوْمُ الْفَصْلِ الَّذِي كُنتُمْ بِهِ تُكَذِّبُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 21
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
احْشُرُوا الَّذِينَ ظَلَمُوا وَأَزْوَاجَهُمْ وَمَا كَانُوا يَعْبُدُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 22
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
مِن دُونِ اللَّهِ فَاهْدُوهُمْ إِلَى صِرَاطِ الْجَحِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 23
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
وَقِفُوهُمْ إِنَّهُم مَّسْئُولُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 24
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
مَا لَكُمْ لا تَنَاصَرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 25
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
بَلْ هُمُ الْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 26
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَى بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 27
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
قَالُوا إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ الْيَمِينِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 28
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
قَالُوا بَل لَّمْ تَكُونُوا مُؤْمِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 29
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَانٍ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَاغِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 30
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَا إِنَّا لَذَائِقُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 31
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
فَأَغْوَيْنَاكُمْ إِنَّا كُنَّا غَاوِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 32
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِي الْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 33
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
إِنَّا كَذَلِكَ نَفْعَلُ بِالْمُجْرِمِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 34
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لا إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 35
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوا آلِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 36
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
بَلْ جَاءَ بِالْحَقِّ وَصَدَّقَ الْمُرْسَلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 37
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
إِنَّكُمْ لَذَائِقُوا الْعَذَابِ الأَلِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 38
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
وَمَا تُجْزَوْنَ إِلاَّ مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 39
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
إِلاَّ عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 40
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
أُوْلَئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 41
Waɗannan sunã da abinci sananne.
فَوَاكِهُ وَهُم مُّكْرَمُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 42
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
فِي جَنَّاتِ النَّعِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 43
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
عَلَى سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 44
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِن مَّعِينٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 45
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
بَيْضَاءَ لَذَّةٍ لِّلشَّارِبِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 46
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
لا فِيهَا غَوْلٌ وَلا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 47
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
وَعِندَهُمْ قَاصِرَاتُ الطَّرْفِ عِينٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 48
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 49
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَى بَعْضٍ يَتَسَاءَلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 50
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
قَالَ قَائِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 51
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
يَقُولُ أَإِنَّكَ لَمِنْ الْمُصَدِّقِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 52
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَامًا أَئِنَّا لَمَدِينُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 53
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 54
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
فَاطَّلَعَ فَرَآهُ فِي سَوَاء الْجَحِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 55
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
قَالَ تَاللَّهِ إِنْ كِدتَّ لَتُرْدِينِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 56
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
وَلَوْلا نِعْمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ الْمُحْضَرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 57
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 58
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
إِلاَّ مَوْتَتَنَا الأُولَى وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 59
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
إِنَّ هَذَا لَهُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 60
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
لِمِثْلِ هَذَا فَلْيَعْمَلْ الْعَامِلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 61
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
أَذَلِكَ خَيْرٌ نُّزُلاً أَمْ شَجَرَةُ الزَّقُّومِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 62
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
إِنَّا جَعَلْنَاهَا فِتْنَةً لِّلظَّالِمِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 63
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِي أَصْلِ الْجَحِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 64
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
طَلْعُهَا كَأَنَّهُ رُؤُوسُ الشَّيَاطِينِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 65
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
فَإِنَّهُمْ لَآكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِؤُونَ مِنْهَا الْبُطُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 66
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 67
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لإِلَى الْجَحِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 68
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
إِنَّهُمْ أَلْفَوْا آبَاءَهُمْ ضَالِّينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 69
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
فَهُمْ عَلَى آثَارِهِمْ يُهْرَعُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 70
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ الأَوَّلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 71
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 72
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
فَانظُرْ كَيْفَ كَانَ عَاقِبَةُ الْمُنذَرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 73
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
إِلاَّ عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 74
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
وَلَقَدْ نَادَانَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ الْمُجِيبُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 75
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
وَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 76
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُ هُمْ الْبَاقِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 77
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الآخِرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 78
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
سَلامٌ عَلَى نُوحٍ فِي الْعَالَمِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 79
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
إِنَّا كَذَلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 80
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 81
Lalle shi, yanã daga bãyinMu mũminai.
ثُمَّ أَغْرَقْنَا الآخَرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 82
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِ لَإِبْرَاهِيمَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 83
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
إِذْ جَاءَ رَبَّهُ بِقَلْبٍ سَلِيمٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 84
A lõkacin da ya je wa dangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَاذَا تَعْبُدُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 85
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
أَئِفْكًا آلِهَةً دُونَ اللَّهِ تُرِيدُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 86
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 87
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
فَنَظَرَ نَظْرَةً فِي النُّجُومِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 88
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 89
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
فَتَوَلَّوْا عَنْهُ مُدْبِرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 90
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
فَرَاغَ إِلَى آلِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلا تَأْكُلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 91
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
مَا لَكُمْ لا تَنطِقُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 92
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًا بِالْيَمِينِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 93
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
فَأَقْبَلُوا إِلَيْهِ يَزِفُّونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 94
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 95
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
وَاللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 96
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
قَالُوا ابْنُوا لَهُ بُنْيَانًا فَأَلْقُوهُ فِي الْجَحِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 97
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
فَأَرَادُوا بِهِ كَيْدًا فَجَعَلْنَاهُمُ الأَسْفَلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 98
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَى رَبِّي سَيَهْدِينِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 99
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
رَبِّ هَبْ لِي مِنَ الصَّالِحِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 100
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
فَبَشَّرْنَاهُ بِغُلامٍ حَلِيمٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 101
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro mai haƙuri.
فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ السَّعْيَ قَالَ يَا بُنَيَّ إِنِّي أَرَى فِي الْمَنَامِ أَنِّي أَذْبَحُكَ فَانظُرْ مَاذَا تَرَى قَالَ يَا أَبَتِ افْعَلْ مَا تُؤْمَرُ سَتَجِدُنِي إِن شَاءَ اللَّهُ مِنَ الصَّابِرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 102
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
فَلَمَّا أَسْلَمَا وَتَلَّهُ لِلْجَبِينِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 103
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
وَنَادَيْنَاهُ أَنْ يَا إِبْرَاهِيمُSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 104
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
قَدْ صَدَّقْتَ الرُّؤْيَا إِنَّا كَذَلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 105
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّ هَذَا لَهُوَ الْبَلاء الْمُبِينُSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 106
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
وَفَدَيْنَاهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 107
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الآخِرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 108
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
سَلامٌ عَلَى إِبْرَاهِيمَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 109
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
كَذَلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 110
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 111
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
وَبَشَّرْنَاهُ بِإِسْحَاقَ نَبِيًّا مِّنَ الصَّالِحِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 112
Kuma Muka yi masa bushãra Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
وَبَارَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَى إِسْحَاقَ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِ مُبِينٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 113
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَى مُوسَى وَهَارُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 114
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
وَنَجَّيْنَاهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ الْكَرْبِ الْعَظِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 115
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
وَنَصَرْنَاهُمْ فَكَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 116
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
وَآتَيْنَاهُمَا الْكِتَابَ الْمُسْتَبِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 117
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
وَهَدَيْنَاهُمَا الصِّرَاطَ الْمُسْتَقِيمَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 118
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِي الآخِرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 119
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
سَلامٌ عَلَى مُوسَى وَهَارُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 120
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
إِنَّا كَذَلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 121
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 122
Lalle, sunã daga bãyinMu mũminai.
وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنْ الْمُرْسَلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 123
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِ أَلا تَتَّقُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 124
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
أَتَدْعُونَ بَعْلاً وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ الْخَالِقِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 125
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
اللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ آبَائِكُمُ الأَوَّلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 126
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 127
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
إِلاَّ عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 128
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِي الآخِرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 129
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
سَلامٌ عَلَى إِلْ يَاسِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 130
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
إِنَّا كَذَلِكَ نَجْزِي الْمُحْسِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 131
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
إِنَّهُ مِنْ عِبَادِنَا الْمُؤْمِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 132
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
وَإِنَّ لُوطًا لَّمِنَ الْمُرْسَلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 133
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ نَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 134
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
إِلاَّ عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 135
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
ثُمَّ دَمَّرْنَا الآخَرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 136
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 137
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
وَبِاللَّيْلِ أَفَلا تَعْقِلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 138
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ الْمُرْسَلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 139
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
إِذْ أَبَقَ إِلَى الْفُلْكِ الْمَشْحُونِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 140
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنْ الْمُدْحَضِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 141
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
فَالْتَقَمَهُ الْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 142
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
فَلَوْلا أَنَّهُ كَانَ مِنْ الْمُسَبِّحِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 143
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
لَلَبِثَ فِي بَطْنِهِ إِلَى يَوْمِ يُبْعَثُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 144
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
فَنَبَذْنَاهُ بِالْعَرَاءِ وَهُوَ سَقِيمٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 145
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
وَأَنبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةً مِّن يَقْطِينٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 146
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
وَأَرْسَلْنَاهُ إِلَى مِائَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 147
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
فَآمَنُوا فَمَتَّعْنَاهُمْ إِلَى حِينٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 148
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
فَاسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ الْبَنَاتُ وَلَهُمُ الْبَنُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 149
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
أَمْ خَلَقْنَا الْمَلائِكَةَ إِنَاثًا وَهُمْ شَاهِدُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 150
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
أَلا إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 151
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
وَلَدَ اللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَاذِبُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 152
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
أَصْطَفَى الْبَنَاتِ عَلَى الْبَنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 153
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 154
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannanhukunci)?
أَفَلا تَذَكَّرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 155
Shin, bã ku tunãni?
أَمْ لَكُمْ سُلْطَانٌ مُّبِينٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 156
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
فَأْتُوا بِكِتَابِكُمْ إِن كُنتُمْ صَادِقِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 157
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
وَجَعَلُوا بَيْنَهُ وَبَيْنَ الْجِنَّةِ نَسَبًا وَلَقَدْ عَلِمَتِ الْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 158
Kuma suka sanya nasaba a tsakãninSa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
سُبْحَانَ اللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 159
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
إِلاَّ عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 160
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 161
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
مَا أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَاتِنِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 162
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
إِلاَّ مَنْ هُوَ صَالِ الْجَحِيمِSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 163
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
وَمَا مِنَّا إِلاَّ لَهُ مَقَامٌ مَّعْلُومٌSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 164
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu, fãce yanã da matsayi sananne."
وَإِنَّا لَنَحْنُ الصَّافُّونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 165
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
وَإِنَّا لَنَحْنُ الْمُسَبِّحُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 166
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
وَإِنْ كَانُوا لَيَقُولُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 167
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًا مِّنْ الأَوَّلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 168
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
لَكُنَّا عِبَادَ اللَّهِ الْمُخْلَصِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 169
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
فَكَفَرُوا بِهِ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 170
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا الْمُرْسَلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 171
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmarMu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
إِنَّهُمْ لَهُمُ الْمَنصُورُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 172
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ الْغَالِبُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 173
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّى حِينٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 174
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 175
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.
أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 176
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَاءَ صَبَاحُ الْمُنذَرِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 177
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّى حِينٍSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 178
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 179
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
سُبْحَانَ رَبِّكَ رَبِّ الْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 180
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
وَسَلامٌ عَلَى الْمُرْسَلِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 181
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
وَالْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَSorah As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) Verse Number 182
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.