Hausa
Sorah Ash-Shuara ( The Poets )

Verses Number 227

طسمSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 1
¦. S̃. M̃.
تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ الْمُبِينِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 2
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
لَعَلَّكَ بَاخِعٌ نَّفْسَكَ أَلاَّ يَكُونُوا مُؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 3
Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
إِن نَّشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِم مِّن السَّمَاء آيَةً فَظَلَّتْ أَعْنَاقُهُمْ لَهَا خَاضِعِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 4
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
وَمَا يَأْتِيهِم مِّن ذِكْرٍ مِّنَ الرَّحْمَنِ مُحْدَثٍ إِلاَّ كَانُوا عَنْهُ مُعْرِضِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 5
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.
فَقَدْ كَذَّبُوا فَسَيَأْتِيهِمْ أَنبَاء مَا كَانُوا بِهِ يَسْتَهْزِؤُونSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 6
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
أَوَلَمْ يَرَوْا إِلَى الأَرْضِ كَمْ أَنبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍ كَرِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 7
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?
إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 8
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 9
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
وَإِذْ نَادَى رَبُّكَ مُوسَى أَنِ ائْتِ الْقَوْمَ الظَّالِمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 10
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
قَوْمَ فِرْعَوْنَ أَلا يَتَّقُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 11
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"
قَالَ رَبِّ إِنِّي أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 12
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
وَيَضِيقُ صَدْرِي وَلا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرْسِلْ إِلَى هَارُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 13
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
وَلَهُمْ عَلَيَّ ذَنبٌ فَأَخَافُ أَن يَقْتُلُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 14
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
قَالَ كَلاَّ فَاذْهَبَا بِآيَاتِنَا إِنَّا مَعَكُم مُّسْتَمِعُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 15
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولا إِنَّا رَسُولُ رَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 16
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."
أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِي إِسْرَائِيلَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 17
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."
قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدًا وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 18
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ الَّتِي فَعَلْتَ وَأَنتَ مِنَ الْكَافِرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 19
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"
قَالَ فَعَلْتُهَا إِذًا وَأَنَا مِنَ الضَّالِّينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 20
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."
فَفَرَرْتُ مِنكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكْمًا وَجَعَلَنِي مِنَ الْمُرْسَلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 21
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
وَتِلْكَ نِعْمَةٌ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنْ عَبَّدتَّ بَنِي إِسْرَائِيلَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 22
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."
قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 23
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
قَالَ رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَالأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا إِن كُنتُم مُّوقِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 24
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُ أَلا تَسْتَمِعُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 25
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ آبَائِكُمُ الأَوَّلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 26
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ الَّذِي أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُونٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 27
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
قَالَ رَبُّ الْمَشْرِقِ وَالْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَا إِن كُنتُمْ تَعْقِلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 28
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
قَالَ لَئِنِ اتَّخَذْتَ إِلَهًا غَيْرِي لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ الْمَسْجُونِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 29
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَيْءٍ مُّبِينٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 30
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
قَالَ فَأْتِ بِهِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 31
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."
فَأَلْقَى عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعْبَانٌ مُّبِينٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 32
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.
وَنَزَعَ يَدَهُ فَإِذَا هِيَ بَيْضَاء لِلنَّاظِرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 33
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.
قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُ إِنَّ هَذَا لَسَاحِرٌ عَلِيمٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 34
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
يُرِيدُ أَن يُخْرِجَكُم مِّنْ أَرْضِكُم بِسِحْرِهِ فَمَاذَا تَأْمُرُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 35
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"
قَالُوا أَرْجِهِ وَأَخَاهُ وَابْعَثْ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 36
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 37
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
فَجُمِعَ السَّحَرَةُ لِمِيقَاتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 38
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.
وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنتُم مُّجْتَمِعُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 39
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?
لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ السَّحَرَةَ إِن كَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 40
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."
فَلَمَّا جَاءَ السَّحَرَةُ قَالُوا لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لأَجْرًا إِن كُنَّا نَحْنُ الْغَالِبِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 41
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"
قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذًا لَّمِنَ الْمُقَرَّبِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 42
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."
قَالَ لَهُم مُّوسَى أَلْقُوا مَا أَنتُم مُّلْقُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 43
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."
فَأَلْقَوْا حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ الْغَالِبُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 44
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
فَأَلْقَى مُوسَى عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 45
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.
فَأُلْقِيَ السَّحَرَةُ سَاجِدِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 46
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
قَالُوا آمَنَّا بِرَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 47
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
رَبِّ مُوسَى وَهَارُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 48
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
قَالَ آمَنتُمْ لَهُ قَبْلَ أَنْ آذَنَ لَكُمْ إِنَّهُ لَكَبِيرُكُمُ الَّذِي عَلَّمَكُمُ السِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ لأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُم مِّنْ خِلافٍ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 49
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."
قَالُوا لا ضَيْرَ إِنَّا إِلَى رَبِّنَا مُنقَلِبُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 50
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
إِنَّا نَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَايَانَا أَن كُنَّا أَوَّلَ الْمُؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 51
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."
وَأَوْحَيْنَا إِلَى مُوسَى أَنْ أَسْرِ بِعِبَادِي إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 52
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne.
فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 53
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.
إِنَّ هَؤُلاء لَشِرْذِمَةٌ قَلِيلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 54
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَائِظُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 55
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَاذِرُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 56
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
فَأَخْرَجْنَاهُم مِّن جَنَّاتٍ وَعُيُونٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 57
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.
وَكُنُوزٍ وَمَقَامٍ كَرِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 58
Da taskõki da mazauni mai kyau.
كَذَلِكَ وَأَوْرَثْنَاهَا بَنِي إِسْرَائِيلَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 59
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.
فَأَتْبَعُوهُم مُّشْرِقِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 60
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
فَلَمَّا تَرَاءى الْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَابُ مُوسَى إِنَّا لَمُدْرَكُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 61
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
قَالَ كَلاَّ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهْدِينِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 62
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
فَأَوْحَيْنَا إِلَى مُوسَى أَنِ اضْرِب بِّعَصَاكَ الْبَحْرَ فَانفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْقٍ كَالطَّوْدِ الْعَظِيمِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 63
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
وَأَزْلَفْنَا ثَمَّ الآخَرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 64
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
وَأَنجَيْنَا مُوسَى وَمَن مَّعَهُ أَجْمَعِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 65
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
ثُمَّ أَغْرَقْنَا الآخَرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 66
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 67
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 68
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
وَاتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَاهِيمَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 69
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَا تَعْبُدُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 70
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"
قَالُوا نَعْبُدُ أَصْنَامًا فَنَظَلُّ لَهَا عَاكِفِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 71
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 72
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
أَوْ يَنفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 73
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
قَالُوا بَلْ وَجَدْنَا آبَاءَنَا كَذَلِكَ يَفْعَلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 74
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
قَالَ أَفَرَأَيْتُم مَّا كُنتُمْ تَعْبُدُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 75
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
أَنتُمْ وَآبَاؤُكُمُ الأَقْدَمُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 76
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"
فَإِنَّهُمْ عَدُوٌّ لِّي إِلاَّ رَبَّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 77
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."
الَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهْدِينِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 78
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
وَالَّذِي هُوَ يُطْعِمُنِي وَيَسْقِينِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 79
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 80
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
وَالَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحْيِينِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 81
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
وَالَّذِي أَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لِي خَطِيئَتِي يَوْمَ الدِّينِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 82
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."
رَبِّ هَبْ لِي حُكْمًا وَأَلْحِقْنِي بِالصَّالِحِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 83
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
وَاجْعَل لِّي لِسَانَ صِدْقٍ فِي الآخِرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 84
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."
وَاجْعَلْنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ النَّعِيمِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 85
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."
وَاغْفِرْ لِأَبِي إِنَّهُ كَانَ مِنَ الضَّالِّينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 86
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
وَلا تُخْزِنِي يَوْمَ يُبْعَثُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 87
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
يَوْمَ لا يَنفَعُ مَالٌ وَلا بَنُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 88
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
إِلاَّ مَنْ أَتَى اللَّهَ بِقَلْبٍ سَلِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 89
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."
وَأُزْلِفَتِ الْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 90
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 91
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ تَعْبُدُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 92
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
مِن دُونِ اللَّهِ هَلْ يَنصُرُونَكُمْ أَوْ يَنتَصِرُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 93
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
فَكُبْكِبُوا فِيهَا هُمْ وَالْغَاوُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 94
Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.
وَجُنُودُ إِبْلِيسَ أَجْمَعُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 95
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
قَالُوا وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 96
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
تَاللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلالٍ مُّبِينٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 97
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
إِذْ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 98
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
وَمَا أَضَلَّنَا إِلاَّ الْمُجْرِمُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 99
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
فَمَا لَنَا مِن شَافِعِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 100
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
وَلا صَدِيقٍ حَمِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 101
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةً فَنَكُونَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 102
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 103
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 104
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَتْ قَوْمُ نُوحٍ الْمُرْسَلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 105
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ نُوحٌ أَلا تَتَّقُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 106
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 107
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 108
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ إِنْ أَجْرِيَ إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 109
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 110
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
قَالُوا أَنُؤْمِنُ لَكَ وَاتَّبَعَكَ الأَرْذَلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 111
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
قَالَ وَمَا عِلْمِي بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 112
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
إِنْ حِسَابُهُمْ إِلاَّ عَلَى رَبِّي لَوْ تَشْعُرُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 113
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."
وَمَا أَنَا بِطَارِدِ الْمُؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 114
"Ban zama mai kõre mũminai ba."
إِنْ أَنَا إِلاَّ نَذِيرٌ مُّبِينٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 115
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."
قَالُوا لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَا نُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمَرْجُومِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 116
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِي كَذَّبُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 117
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
فَافْتَحْ بَيْنِي وَبَيْنَهُمْ فَتْحًا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِي مِنَ الْمُؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 118
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
فَأَنجَيْنَاهُ وَمَن مَّعَهُ فِي الْفُلْكِ الْمَشْحُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 119
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ الْبَاقِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 120
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.
إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 121
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 122
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
كَذَّبَتْ عَادٌ الْمُرْسَلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 123
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلا تَتَّقُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 124
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 125
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 126
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ إِنْ أَجْرِيَ إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 127
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."
أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ آيَةً تَعْبَثُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 128
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 129
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"
وَإِذَا بَطَشْتُم بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 130
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 131
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَاتَّقُوا الَّذِي أَمَدَّكُم بِمَا تَعْلَمُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 132
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."
أَمَدَّكُم بِأَنْعَامٍ وَبَنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 133
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
وَجَنَّاتٍ وَعُيُونٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 134
"Da gõnaki da marẽmari."
إِنِّي أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 135
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."
قَالُوا سَوَاء عَلَيْنَا أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُن مِّنَ الْوَاعِظِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 136
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."
إِنْ هَذَا إِلاَّ خُلُقُ الأَوَّلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 137
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko."
وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 138
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
فَكَذَّبُوهُ فَأَهْلَكْنَاهُمْ إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 139
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 140
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَتْ ثَمُودُ الْمُرْسَلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 141
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ صَالِحٌ أَلا تَتَّقُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 142
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 143
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 144
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ إِنْ أَجْرِيَ إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 145
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."
أَتُتْرَكُونَ فِي مَا هَاهُنَا آمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 146
"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 147
"A cikin gõnaki da marẽmari."
وَزُرُوعٍ وَنَخْلٍ طَلْعُهَا هَضِيمٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 148
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"
وَتَنْحِتُونَ مِنَ الْجِبَالِ بُيُوتًا فَارِهِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 149
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 150
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَلا تُطِيعُوا أَمْرَ الْمُسْرِفِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 151
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."
الَّذِينَ يُفْسِدُونَ فِي الأَرْضِ وَلا يُصْلِحُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 152
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."
قَالُوا إِنَّمَا أَنتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 153
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."
مَا أَنتَ إِلاَّ بَشَرٌ مِّثْلُنَا فَأْتِ بِآيَةٍ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 154
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
قَالَ هَذِهِ نَاقَةٌ لَّهَا شِرْبٌ وَلَكُمْ شِرْبُ يَوْمٍ مَّعْلُومٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 155
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
وَلا تَمَسُّوهَا بِسُوءٍ فَيَأْخُذَكُمْ عَذَابُ يَوْمٍ عَظِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 156
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."
فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا نَادِمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 157
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
فَأَخَذَهُمُ الْعَذَابُ إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 158
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 159
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ الْمُرْسَلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 160
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلا تَتَّقُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 161
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 162
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 163
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ إِنْ أَجْرِيَ إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 164
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
أَتَأْتُونَ الذُّكْرَانَ مِنَ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 165
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"
وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمْ رَبُّكُمْ مِنْ أَزْوَاجِكُم بَلْ أَنتُمْ قَوْمٌ عَادُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 166
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"
قَالُوا لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَا لُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمُخْرَجِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 167
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ الْقَالِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 168
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
رَبِّ نَجِّنِي وَأَهْلِي مِمَّا يَعْمَلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 169
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
فَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 170
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
إِلاَّ عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 171
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.
ثُمَّ دَمَّرْنَا الآخَرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 172
Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.
وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِم مَّطَرًا فَسَاء مَطَرُ الْمُنذَرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 173
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 174
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 175
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
كَذَّبَ أَصْحَابُ الأَيْكَةِ الْمُرْسَلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 176
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.
إِذْ قَالَ لَهُمْ شُعَيْبٌ أَلا تَتَّقُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 177
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 178
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
فَاتَّقُوا اللَّهَ وَأَطِيعُونِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 179
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ إِنْ أَجْرِيَ إِلاَّ عَلَى رَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 180
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
أَوْفُوا الْكَيْلَ وَلا تَكُونُوا مِنَ الْمُخْسِرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 181
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."
وَزِنُوا بِالْقِسْطَاسِ الْمُسْتَقِيمِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 182
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."
وَلا تَبْخَسُوا النَّاسَ أَشْيَاءَهُمْ وَلا تَعْثَوْا فِي الأَرْضِ مُفْسِدِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 183
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."
وَاتَّقُوا الَّذِي خَلَقَكُمْ وَالْجِبِلَّةَ الأَوَّلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 184
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
قَالُوا إِنَّمَا أَنتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 185
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."
وَمَا أَنتَ إِلاَّ بَشَرٌ مِّثْلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ الْكَاذِبِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 186
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."
فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفًا مِّنَ السَّمَاء إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 187
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."
قَالَ رَبِّي أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 188
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ الظُّلَّةِ إِنَّهُ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 189
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
إِنَّ فِي ذَلِكَ لآيَةً وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 190
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 191
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
وَإِنَّهُ لَتَنزِيلُ رَبِّ الْعَالَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 192
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
نَزَلَ بِهِ الرُّوحُ الأَمِينُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 193
Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.
عَلَى قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ الْمُنذِرِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 194
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.
بِلِسَانٍ عَرَبِيٍّ مُّبِينٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 195
Da harshe na Larabci mai bayãni.
وَإِنَّهُ لَفِي زُبُرِ الأَوَّلِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 196
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
أَوَلَمْ يَكُن لَّهُمْ آيَةً أَن يَعْلَمَهُ عُلَمَاء بَنِي إِسْرَائِيلَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 197
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?
وَلَوْ نَزَّلْنَاهُ عَلَى بَعْضِ الأَعْجَمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 198
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,
فَقَرَأَهُ عَلَيْهِم مَّا كَانُوا بِهِ مُؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 199
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.
كَذَلِكَ سَلَكْنَاهُ فِي قُلُوبِ الْمُجْرِمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 200
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
لا يُؤْمِنُونَ بِهِ حَتَّى يَرَوُا الْعَذَابَ الأَلِيمَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 201
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.
فَيَأْتِيَهُم بَغْتَةً وَهُمْ لا يَشْعُرُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 202
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
فَيَقُولُوا هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 203
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 204
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?
أَفَرَأَيْتَ إِن مَّتَّعْنَاهُمْ سِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 205
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
ثُمَّ جَاءَهُم مَّا كَانُوا يُوعَدُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 206
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
مَا أَغْنَى عَنْهُم مَّا كَانُوا يُمَتَّعُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 207
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.
وَمَا أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلاَّ لَهَا مُنذِرُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 208
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.
ذِكْرَى وَمَا كُنَّا ظَالِمِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 209
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
وَمَا تَنَزَّلَتْ بِهِ الشَّيَاطِينُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 210
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
وَمَا يَنبَغِي لَهُمْ وَمَا يَسْتَطِيعُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 211
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
إِنَّهُمْ عَنِ السَّمْعِ لَمَعْزُولُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 212
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
فَلا تَدْعُ مَعَ اللَّهِ إِلَهًا آخَرَ فَتَكُونَ مِنَ الْمُعَذَّبِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 213
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
وَأَنذِرْ عَشِيرَتَكَ الأَقْرَبِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 214
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
وَاخْفِضْ جَنَاحَكَ لِمَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 215
Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
فَإِنْ عَصَوْكَ فَقُلْ إِنِّي بَرِيءٌ مِّمَّا تَعْمَلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 216
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
وَتَوَكَّلْ عَلَى الْعَزِيزِ الرَّحِيمِSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 217
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
الَّذِي يَرَاكَ حِينَ تَقُومُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 218
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 219
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
إِنَّهُ هُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 220
Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani.
هَلْ أُنَبِّئُكُمْ عَلَى مَن تَنَزَّلُ الشَّيَاطِينُSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 221
Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
تَنَزَّلُ عَلَى كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٍSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 222
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.
يُلْقُونَ السَّمْعَ وَأَكْثَرُهُمْ كَاذِبُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 223
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
وَالشُّعَرَاء يَتَّبِعُهُمُ الْغَاوُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 224
Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.
أَلَمْ تَرَ أَنَّهُمْ فِي كُلِّ وَادٍ يَهِيمُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 225
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
وَأَنَّهُمْ يَقُولُونَ مَا لا يَفْعَلُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 226
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?
إِلاَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَذَكَرُوا اللَّهَ كَثِيرًا وَانتَصَرُوا مِن بَعْدِ مَا ظُلِمُوا وَسَيَعْلَمُ الَّذِينَ ظَلَمُوا أَيَّ مُنقَلَبٍ يَنقَلِبُونَSorah Ash-Shuara ( The Poets ) Verse Number 227
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.