Hausa
Sorah Al-Humazah ( The Slanderer )

Verses Number 9

وَيْلٌ لِّكُلِّ هُمَزَةٍ لُّمَزَةٍSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 1
Bone ya tabbata ga duk mai nune, mai zunɗe (mai raɗa).
الَّذِي جَمَعَ مَالا وَعَدَّدَهُSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 2
Wanda ya tara dũkiya, kuma ya mayar da ita abar tattalinsa.
يَحْسَبُ أَنَّ مَالَهُ أَخْلَدَهُSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 3
Yana zaton cẽwa dũkiyarsa za ta dawwamar da shi.
كَلاَّ لَيُنبَذَنَّ فِي الْحُطَمَةِSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 4
A'aha! Lalle ne zã a jẽfa shi a cikin Huɗama.
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْحُطَمَةُSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 5
Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa Huɗama?
نَارُ اللَّهِ الْمُوقَدَةُSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 6
Wutar Allah ce wadda ake hurawa.
الَّتِي تَطَّلِعُ عَلَى الأَفْئِدَةِSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 7
Wadda take lẽƙãwa a kan zukata.
إِنَّهَا عَلَيْهِم مُّؤْصَدَةٌSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 8
Lalle ne ita abar kullẽwa cea kansu.
فِي عَمَدٍ مُّمَدَّدَةٍSorah Al-Humazah ( The Slanderer ) Verse Number 9
A cikin wasu ginshiƙai mĩƙaƙƙu.