Hausa
Sorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour )

Verses Number 11

الْقَارِعَةُSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 1
Mai ƙwanƙwasar (zukata da tsõro)!
مَا الْقَارِعَةُSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 2
Mẽnẽ ne mai ƙwanƙwasa?
وَمَا أَدْرَاكَ مَا الْقَارِعَةُSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 3
Kuma me ya sanar da kai abin da ake ce wa mai ƙwanƙwasa?
يَوْمَ يَكُونُ النَّاسُ كَالْفَرَاشِ الْمَبْثُوثِSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 4
Rãnar da mutãne za su kasance kamar 'ya'yan fari mãsu wãtsuwa.
وَتَكُونُ الْجِبَالُ كَالْعِهْنِ الْمَنفُوشِSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 5
Kuma duwãtsu su kasance kamar gãshin sũfin da aka saɓe.
فَأَمَّا مَن ثَقُلَتْ مَوَازِينُهُSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 6
To, amma wanda ma'aunansa suka yi nauyi.
فَهُوَ فِي عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 7
To, shi yana a cikin wata rayuwa yardadda.
وَأَمَّا مَنْ خَفَّتْ مَوَازِينُهُSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 8
Kuma amma wanda ma'aunansa suka yi sauƙi (bãbu nauyi).
فَأُمُّهُ هَاوِيَةٌSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 9
To, uwarsa Hãwiya ce.
وَمَا أَدْرَاكَ مَا هِيَهْSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 10
Kuma me ya sanar da kai mece ce ita?
نَارٌ حَامِيَةٌSorah Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) Verse Number 11
Wata wuta ce mai zafi.